Namiji Baya Kadan
Page 6
Juyowa ya kuma yi gareta tare da tsura mata ido, Itama idon ta zuba mai tare da cewa "aha inajin ka" A hankali ya kara rege tafiyar tare da maida hankali shi gareta cikin tsareta da ido yace. "Khadija gobe fa zanyi Aure".
Da sauri ta cilla mai harara tare da tabe baki ta kuma juyo cikin yanayin kai yaro ne tace. "Auren ai ba wasan yara bane kuma ba iya zance bane bare kace ka iya kai yanzu ko nauyin kalmar bakaji ba? Tun da ta fara mgn ya tsura mata ido bakinta kawai yake kallo sai da tai shiru sannan yace.
ki shiga taitayinki fa da gaya min duk mgnar da tazo bakinki wallahi zaki kona kanki ina gaya miki ki kama bakinki da cemin yaro tam. Toh fa Sannu yayana ai kam dole nace yaro kai ba yaron bane, sai ta kuma sa dariya ta nunashi da yatsa sai ta kuma dariya tana fadin. kalle ka fa yaro ko rinka baka faraba bare ka gama wai shine harda wani zakayi Aure Amman dai sai in Yar kauye zaka Aura ko? yar 12 years kai wlh kai kam ma ba wanda zai baka yarsa.
Dariya take sosai tana fadi mai abinda bai sonji. Cikin tunzura ya damko hannu ta ya matse da karfi har saida taji hannun ya bada sauti das sannan zafi ya ratsata har saida ta zaro ido woje tare da cewa.Wayyo hannuna kai Mahmoud karyani zakayi ka sake min hannu kaji mugunta dan na fadi gaskiya. Shi kuwa ido ya tsura mata sannan ya kara matsota yana mai piki-piki da ido tuni fuskarsa ta juya kara matsota yayi har kamar zai danneta jikin marfin motar murya na rawa yace.
Ita kuwa cikin jin zafin yadda ya matan da takaici wannan wanne irin rainine ko iskanci hannu tasa ta hankadeshi amman ta kasa kwatar kanta cikin takaicin tace. Me haka Mahmoud ban son iskanci ni Sa'arkace ko rashin kunya zaka nuna min aikin banza yaro dan kaga ana wasa da kai sai kuma raini ya shiga. Kicini ya take ta kwace kanta amman ta kasa sai shi da kanshi ya saketa tare da juyawa ya kalli titi. Habawa ita kam Khadija fada take kamar ta mareshi dan ya cikata tab.
Shi kuwa shiru yayi yana tuki sai zufan da ya keto mai duk da sanyin AC hannu yenshi kab rawa suke. So yake yayi mgn Amman kuma ya kasa bazai iyaba ko yace zai maganar zatake fita da i ina shiyasa sai kawai ya kame lips inshi na k'asa yai ta tsotsa yana jinta tana ta bala'i harda cewa.
Ai kai dole amaka Auren tun baka jamana abin kunya ba aikin banza aikin wofi.
Shi kam bai kulaba har suka dawa ana bud'e musu gate yana shiga ko parking bai karisa yiba ta kama kokarin bude mota zata fita shiko komawa yayi ya jingina jikin sit sai numfashi yake fiddawa cikin sanyi.
Cikin fada tace."Ka bude min in fita dan ina da abinyi"Cikin wani irin murya yace .
Cikin isa yace."Allah in kika yadda kika tab'ani wallahi zakisha matsa, ba abinda kika iya sai baki ai tida kince ban fara rinka bama bare Na gama, ako bai kamata ki kasa kwace kanki a hannuna ba"Komawa tayi ta zauna danji zai kuma matseta cikin hade fuska tace.
Ajiyar zuciya Anty tayi tare da cewa "har naji tsoro kar bai d'inka ba"Dariya sukayi tare da kwanciya.
Da safe misalin karfe 11 kofar gidan Alhj Ibrahim cike yake mak'il da Al'ummar Annabi manyan mutanen masu fada aji da malamai manya da matasa da yara tako ina a cike ake. Haka kuwa cikin gidama makil yake yan uwa da abokan arziki.
Su Khadija an tasa Amira a gaba dasu Fatima suna ta mata tsiya ita ko tuni ta nemi idannunta. Cikin juyawar iska sautin d'aura Auren _Mahmoud Ibrahim Mahmoud da _ Khadija Sani Mahmoud ya ratsa kunnuwan illahirin mutanen dake cikin gidan cikin mamaki da Al'ajabi aka rinka kallo kallon juna. Cikin sanyi Goggo Zahra dake gefe tace.
Alhamdulillah Allah ya sanya Alkhairi Mahmoudu Allah ya tayaka riko.
Rayhana ce cikin kad'uwa tace."Goggo Wai wanne Mahmoud dinne yayi Aure kuma da wacce Khadijan. Lokaci daya kuma Aysha ma tace."Nima an daure min kai Wai da gske Mahmoud ne yayi Auren. Mami ce ta fito cikin bakin ciki da hade fuska da takaici taje gaban Goggo Zahra cikin fushi kamar zatayi kuma tace. fisabilillahi Zahra yayanki yayi mana adalci ace ina Mahmoud ina Aure kuma ko Aure zaiyi ai sai a nema mai dai-dai dashi ina Khadija ina Mahmoud.
Sai kuma kuka mai karfi ya kofce mata fad'a wa jikin Goggo Zahra tayi cikin kuka mai tsuma rai da kaji kasan zuciyar mai yinshi cike yake da takaici. Cikin kukan ta rike hannun Goggo Zahra ta kalleta fuska duk hawaye tace."Goggo Zahra ase yanzu Dan Allah ya jarabceni da mutuwar Aure sai a maidani tamkar yar kaza Goggo Zahra a rasa Wanda za'a cusamin sai Mahmoud yaro k'arami Goggo yanzu su Abba ne suka min haka me Na aikata musu da zasu hukuntani da haka.
Ita kam Khadija zuwa yanzu duhu ya rufe mata ido lokaci d'aya ta fara jin jiri. Kalaman, Mami yasata ta kara rudewa.
Cewa take "Ji muna furci ai da saninki bake kikace kar a gayawa kowa ba Dan gulma yanzu kice baki saniba.
Cikin kuka tace." Wallahi Mami ban saniba wlh bada yardana akayi ba ".
Sai Kuma ta zame tayi k'asa cikin....top.
Page 7
Bani da lokacin ku bare nace naji zafin zantu kanku a kaina zaginku kanku zai koma abinda na sani baku da damar dakatar dani akan harkar nan na rubuce-rubuce baku isaba dan baku kuka saniba kuma bansa ko wacce karantawa a doleba kuma bazan FASA abin danayi niya ba fans Na muje zuwa ga Mahmoud on top.
Zamewa kan gado tayi tare da kife kanta cikin pillows ta saki kuka mai tsuma rai tana kukanne har numfashinta na fizga, Goggo Zahra yace ta matso kanta cikin sanyi tace.
Haba Khadija Aure fa akayi muku ba zaman banza ba Mahmoud fa dan uwanki ne shin akwai abinda baki sani bane a yanzu ba abinda ya rage face kiyi biyeyya ga Allah da manzonsa sai kuma kiyiwa iyayenkin da'a kiyiwa mijinki biyeyyah.
Ayyah Khadija kibar kukan nan haka zai cutar da ke, Aurene an rigada a d'aura bamu da wani abin yi a kai ni Na fahim ceki, Kiyi hakuri da Abinda Mami tace miki insha Allah itama zata fahimta.
Kanta ta dago cikin muryar kukan tace."Ni na tsani Mahmoud bana kaunar ganin shi sabida ya cuceni ya min karya sannan ya hada min sherri. Fatima dake tsaye gefe cikin jin zafin furu cin da tayi Na cewa ta tsani Mahmoud ta dan ja tsaki tare da cewa.
Toh sai me ki tsaneshin mana ai Uwarsa da mukam muna sonshi. Tana kaiwa nan ta fice abinta. Anty ce ta bita da ido cikin mmk sannan ta kalli Goggo Zahra tace. Ni tsoro naji kar Auren nan ya haddasa mana fitina a family. Mikewa Goggo Zahran tayi cikin cewa. insha Allah sai Alkhairi, Shi kuwa Mahmoud A kofar gida hatta ya Auwal mmk ya rinkyi yana bin kanin nashi da ido shi da zugar abokanshi, shi dai yabar batun Auren Khadija tun randa iyayen Nazir sukazo Abba yace musu, ya mata miji sannan ya basu hak'uri, ase dama Mahmoud ne mijin.
Shiko Mahmoud Yau itace ranar farin cikinsa gaba daya bakinshi ya kasa rufuwa gashi yayi fita ta alfarma ya fito a Mahmoud on top manyan kaya ya saka harda gare shaddace yar asali kalan sararin samaniya sannan yasa hula fara sai takalmi shima fari Sai agogon Daimon dake makale a hannu shi farar fatarsa ta taimaka wurin fiddashi gashin kanshi nan duk ya konto ta k'eyarsa sai kamshi yake zubawa yana taku cikin k'asaita sai fatan Alkhairi ake mai hatta manyan mutane sai sumika mai hannu suna mai Addu'ar Allah tayashi riko.
Amin suka amsa baki d'aya, Mami ce ta kalli Mahmoud din cikin hade fuska tace. Mahmoud matsayin na kenan ina mahaifi yarka Amman har kayi neman Aure cikin muna furci duk ban saniba wato kana da wata uwar da tafini ko. Cikin sanyi ya dan ja jikinshi ya matsota kanshi ya dan daura kan cinyarta tareda cirehular kanshi.
Murya a sanyaye yace."Kimin afuwa Mami na Auren ne ya kama ni dole wallahi bazan iya rayuwa ba mata ba ina da buk'atar mace a rayuwa ta shiyasa Mami Na ba boye miki nayi ba Abba ne yace a bari sai Abu ya tabbata sannan kuma kin sani, Annabinmu da kanshi yace A suturta nema a bayyana samu. Duk parlon shiru sukayi duk kunya ta rufe su shiko ko a jikinshi, Haka Abba yai ta musu nasiha har duk suka fahimci illar dake cikin hana shi yin Auren, Shi kuwa Mahmoud cikin rada ya matsota gun Anty Rayhana a hankali yace, Anty Ray ina Matata ban ganta ba hankali na ya bar jikina.
Cikin sanyi itama ta bashi labarin halin da Khadijan ke ciki. Lokaci daya fuskarsa ta sauya shi da kanshi yasan yayiwa Khadynshi laifi gashi bai son bacin ranta, Suna fita parlon kai tsaye cikin gida yayi aiko yan uwa da abokan wasa sukayi caa a kanshi suna, Masha Allah kaga yaro mai kamshin angwaye Mahmoud on top kenan Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafaya. Shi kuwa murmushi kawai yake dan yi tare da cewa Amin. Ita kuwa tana jinshi ya shigo parlon Anty ta tashi cikin jin jirin ta rufe kofar sannan ta zame a wurin cikin jin tsanarsa a ranta.
Anty Rayhana tai ta kiranta ta bude taki, Cikin sanyi yace "Anty Ray barta"Sai ya juya ya shiga dakin Mami ananma kanneta sunyi ta mai fatan Alkhairi yayinda wasu ke mai kallon ya d'ebo dala ba gammo.
Ya fita dakinshi ya shige cikin karfin hali ya ja woyarsa number ta ya tsurawa ido sannan a hankali ya dannan Calling. Ita kuwa tana dakin tayi kukan har ta gaji ta koma ta konta cikin tsiyayar da kollah, A hankali taji woyarta Na suwa bata dagaba har ta tsinke a haka har kusan 5 miss call Sannan ta rinka jin sautin shigar text message a nanne ta jawo woyar tana dubawa tabta shine sai kawai ta saki kuka tare da cillah woyar gefe.
Kuka mai cin rai ta kuma saki jin Wai Mahmoud ke kiranta Matata Wai shi kuma mijin ta. Shi kuwa kukan ya kara tunzuroshi baiki ace tana kusa dashiba da ya tabbata zai tsaida kukan.
Mami ce ta leko cikin fada tace "wai ko baza'a bada kayan banne, cikin dishewar murya tace." Ayyah Mami kayan suna gun shine fa" Fatima ta karbo mana.
Baki fatiman ta tabe cikin takaici tace."Wallahi bazan kuma zuwa ba naje kusan sau 3 yace bazai bayarba in mun damu kije. Cikin cika da takaici tace. Toh wallahi sai dai mu hak'ura Dan bazan jeba.
Anty ne tace. Ke harda wallahi hinki to wallahi maza mike ki karbo kinaga tun d'azu Amira ta shirya ke ake jira duk wuri ya cika.
Jin motsin mutune a bayanta yasa ta juyo da sauri ganin shi ya sata sai hawaye shar a ranta take cewa yanzu d'an yaron nanne za,ace mijin ta.
Kanta ya nufa itako ganin haka yasa ta rinka Jan baya-baya har ta fada kan 3 stirs A hankali ya zauna gefenta cikin tsura mata ido yasa hannu zai jawota tai maza ta buge hannu ganin haka yasa cikin isa ya fizgota jikinshi ya matsota a kirjinshi cikin sauke numfashi ya tallabo kanta murya da jikinshi na rawa yasa hannushi ya....
contact-fom
0 Comments