f Mijin Babata Ne 31 to 56

Mijin Babata Ne 31 to 56

 

Mijin Babata Ne 31 to 56


PAGE 31 TO 40

Sallama sukayi ma juna bayan an samu mai kula da Abba namiji,zai biyashi. Kai tsaye gida ya wuce daga farfajiyan gidan ya gane hajiyar gidan bata dawo ba,taÉ“a baki yayi da girgiza kai cike da takaici. ÆŠakin shi ya wuce kai tsaye,bayan ya aje key da wayoyin shi ya cire kaya,ya shiga toilet ya watso ruwa tare da É—auro alwala,yai shafa'i da wutiri,kayan baccin sa ya saka ya hau gado ya É—au wayar shi yafara dannawa. Sai 10:30pm yajiyo shigowan ta ta Æ™ure  waÆ™a a motor kamar club.MGirgiza kai yayi cike da takaici,watou a tinanin tafiyar kwana  yayi shiyasa taje tai dare,Æ™wafa yayi. Itako sam bata kula da motor shiba tafito ta wuce ciki riÆ™e da takeaway É—in da tayi order.







ÆŠakin kaca kaca da kaya gefe ta aje  ta cire kayan ta watsar a gefe, tura kayan da ke kan gadon tayi gefe ta hau ta zauna bata damu da tayi wanka ta canja kaya ba, bude takeaway É—in tayi tafara cin abinta tana danna waya hankalin ta kwance. Washagari tunda sassafe ya tashi nufi gidan Ummien sa,basu tashi ba ya zauna a pallow suna ta hira da Iya mai ma Ummy girki, tun yana yaro suke tare da Iya ke gidan, tana da kirki ga tsafta tare da halin dattako, sam bata nuna kwaÉ—ayi a abinda ba abata ba. Umurni yabata tamai girki yana da marasa lafiya a asbiti baban wai course mate É—in  shi,aiko a mintina Æ™alilan ta haÉ—a musu breakfast, harta gama ya É—auka ya tafi dashi, su Cutie basu tashi ba.

Abba yafara kai mawa,ya farka amma yana kwance sai bin Aliyu da ido yake ,yana mamaki, yana so ya motsa bakin shi ya tambaye shi ina Jidda amma ba dama sau hawaye. Aliyu aje kwandon yayi jiki na rawa ya ƙarasa jikin gadon yana faɗin,"subhanallah Abba hawaye kuma mai yafaru. Kallo wanda ya kwana da Abba yayi,yace,"ya jikin nasa. Ɗan dattijon gyara zama yayi yace,"alhamdulillah, daya farka na kira Likita ya duba shi, an ƙara mai allura. "Masha Allah ubangiji ya ƙara masa lafiya. "Ameen ya Allah. "Ga abinci nan na kawo ma, zanje in duba ƙanwata da take gida".

To É—annan Allah yayi albarka. Amin ya amsa dashi, kafin yakai duban shi ga Abba dashi yake kallo,har yanzun amma hawayen ya tsaya yace,"Jiddah itama tana Æ™arÆ™ashin  kulawan likitoci, jikinta taji sauÆ™i, yanzun haka zanje wajan sune, Allah ya baka lafiya zanje indawo. Cikin murya  Æ™asa Æ™asa mai cike da tarin ladabi yake maganan, yana gamawa yai ma mai kula da Abban sallama ya wuce. Jidda ko É“angaren ta Æ™arfe uku da wasu mintoci ta wani farka a razane tana kira Abba Abba Abba, can cikin bacci Tani ta jiyo ta ta tashi a razane take Hansai  da tayine yai sanadiyan tashin ta.







Idon ta arufe yake tana kiran Abba. Tani riƙe mata hannuwa tayi tana faɗin sannu Jiddah kin farka. Cike da kulawa take maganan. Muryan da tajine yasata waye manyan idanuwan ta da sukayi mata nauyi. Ganin su Hansai yasa take mamakin,kallo tafara bin ɗakin dashi,daga gani nan ba ƙauyen su bane,ya akayi tazo nan waya kawo ta. Hansai tace, sannu Jidda Kulu bari akira Likita. Da mamaki take kallon Hansai nan asibiti ne to mi ya faru waya kawota nan.

Hansai jiki na rawa taje ta kira Likita suka dawo tare. Dudduba ta yayi, kafin yai mata tambayoyi  yace,"ya sunan ki. Ahankali ta buÉ—e baki tace,"Jiddah. Good yace, yana gyaÉ—a kai, ya nuna Hansai yace yasunan wannan. Kallonta takai gareta tsawon minti É—aya, tace," Hansai, wancan kuma Tani duk yan Æ™auyen mune, ina Abba na, wake kula dashi ,mai ya kawo ni nan. AruÉ—e take magana tana kallon 

Dr. Gyara murya yayi yana murmishi yace,

PAGE 41 TO 45

Gyara murya yayi yana murmushi yace," Alhamdulillah, ta maganganun ta nagano bata da matsalan Æ™waÆ™walwa,nan asbiti ne,Hauwa, Abban ki na gida. Cikin tattausan murya yake mata magana. Hansai ta amsa da cewa,"Ali É—an gidan Abban ki Aminu,ya É—auko Abban ki ya kaishi asbiti shima. Sauke nauyayyam ajiyar zuciya tayi kafin ta É—uÆ™ar dakai tace, "Alhamdulillah" duk da ambaton Aliyu saida ya faÉ—ar mata da gaba. Dr tambayoyi yai mata cike da Æ™warewa irin nasu na Likitoci tana bashi amsa,daga bisani yasa aka kawo mai allura    yai mata take bacci ya Æ™ara É—aukan ta. karfe bakwai da tan mintoci ta kuma farkawa, da salati bayan nan tayi addu'an tashi daga bacci,kana ta miÆ™e ta zauna,tanabin ruwan da ke tafiya cikin hannun ta da kallo.






Tani ta taso da hanzari tace,"sannu JIDDA, ya jikin. "Alhamdulillah", ta amsa dashi murya kasa kasa. To to Allah ya ƙaro dama". Amin", ta amsa dashi a taƙaice. Ko akira likitane. Tani ta ƙara tambaya. A temaka min zaki in rama sallolin da ake biyata". Da mamaki Hansai ta riƙe baki ganin karfin hali wai sallah zatayi, ita in tana ciwo ai bata rama sallah, lafiya ƙalau ma bata dameta ba,sai taga idon mutane takeyi, taɓa baki tayi kana daga bisani tace,"to bari intemaka miki, baki bari karnan jikin ki har ya ƙara ƙarfi.

Ta ƙarashe maganan da sigar tambaya. Ahankali ta girgiza kanta,kana tace,"ke Tani inna mutu fa, inje ince ma Allah maine? ince banji sauki ba. Lokaci ɗaya ta jero mata wa yannan tambayoyin. Mamaki Tani take yar ƙaraman yarinya da magana babba, yarinyar nan dai wuni take talla,ya akayi tasan karatun islamiya. Abinda ko ke faruwa, inde Jidda ta ɗau tallan goro da yamma, can gidan fura take tafiya,su suna da yawan islamiyoyi da boko, jikin wata islamiya take zama tana sauraran karatun su, anan duk ta iya abu buwa da yawa,tana sha'awan karatun addini,amma ita talla bazai bari tayi ba,kullum tana ti-ti yawon talla. "Temaka min manaTani".

Ta ƙara magana,muryanta ciki ciki. Tani sa hannu tayi ta tallafo haɓanta, suka taka ahankali harcikin banɗakin ta barta tafito don ta kama ruwa tayo alwala, tace mata inta ida ta kirata, hakan ko akayi tana idawa ta buɗo ƙofa ta kirata, kamata tayi takaita kan kallabin ta da ta shimfiɗa ta zaunar da ita tabata hijjab ɗinta ta saka. Rama salloli tafarayi tun na jiya har yau. Zarah jiki yayi tsami yayi laushi,bata ƙara tabbatar da yan sanda basu da imani basu da mutunci ba,saida Aliyu yazo ya basu kuɗi, suka ƙara ƙaimi amata rashin mutunci. Duk tayi laushi,dana sanin abinda tayi takeyi yanzun da yanzun tana gida tana juya biyar ta zama goma.







Da tabari ta shigo ta same ta da icen dalbejiya ta jibga babu mai ce mata kanzil,Allah ya tsine ma Hansai take faÉ—a a zuciyarta. Duk da haka bata saduda ba, jira take ta fita,duk wahalar da aka bata anan sai ta fanshe ajikin JIDDAH.

Uban dame suke tiƙawa a tsakanin su,mutane sun taru ana raba su amma sam basa ji, har yakai da mutane sun koma kallon su. "Shegiya karuwa, karuwan cina yamin rana tunda ni ina iya sayan sabulu kizo ki ɗauke kina wanka". Fadan Atika datake ta huci kamar maciji. "Karuwa gakinan ƙatotuwar ashawo ciki nawa kika zubar. Faɗar Sa'ina da take ƙoƙarin cakumo Atiƙa,dakyar aka shiga tsakanin su,amma basu dena cin mutuncin juna ba da bacin su.

NIKO NACE ALLAH YA WADARAN RAKUMIN DAWA YAKI ƳAƳA.

"Shegiya yar iska ke Saminu da ya kawo dukiyar auren ki, ina ce har ubanshi kike lalata dashi. Fadan Atikah da har yanzun huci take tana zare Æ™ananun ido irin na uwarta. Mutanan wajan salati suka É—auka cike da mamaki. Take dambe ya kara kaurewa tsakanin sun suna yaga ma juna kaya. Dakyar aka raba su, akaja Sa'ina akayi waje da ita. Asafiyar ranan ko, kauyen nan labarin su  ake lungu da saÆ™o. Turo Æ™ofar da akayine yasa dukan su suka É—ago kai.............!

PAGE 46 TO 56

Kafin ya wuce da ita gidan Ummie gaban shi na fadi, yan a tunanin draman da zasu kwahe da Ummy sa. Ko da suka isa yace,"mata ta fara shiga ciki,fita tayi jiki a sanyayye ta nufi cikin gidan, don rabon da tazo gidan tun bikin Aliyu da sukazo da Abban ta da zai daura ma Aliyu aure,ana gama daurin auran suka koma Æ™auye  tun da  suka koma Abban ta ya fadi tun daganan ya kama ciwo. Ahankali ta tura Æ™ofar tashiga da" asallamualaikum. Cikin sanyin murya tayi maganan can Æ™asa Æ™asa. 









Waalaikumusalam. Ummy dake daura ma Cute ɗan kwali, ba tare da ta dago ba. Jin shiru ba'a ƙara magana ba ba'a shigo ba yasata ɗago kai, karaf idon su ya sarke da juna, da mamaki Ummy ke kallon ta, yau ne rana na farko da taganta cikin shiga mai kyau, don kullum zata ganta cikin duƙu duƙun kaya, taso ta temaka mata amma masifar ZARAH ya hana ta temake ta, tunda ALIYU ya watsa mata ƙasa a ido, cikin ma wuyacin halin da take ganin ta bai mata daɗi yana ɗaga mata hankali yasa tadena zuwa Lafani.

Lokaci dya ta fadada murmushin ta mai nuna alamun tsan tsan farin ciki ganin ta tace,"a'a Hauwa Jidda ce agidan namu yau lalle marhaban, ina Ibrahim din, ki shigo ma kin coge jikin Æ™ofa kamar baÆ™uwa". Murmushi tayi  tana sunkuyar da kai ta Æ™araso cikin falon ta zauna a Æ™asa. Keko Jidda wannan halin naki na Æ™auyawan fulani nanan,sai wani noke jiki kikeyi kamar wata kifi. Kwallahiya Ummy. Lafiya lau ya kike, kitashi  ki zauna kan kujera. Girgiza kai, Jidda tayi tana tura shi cikin hijjab. " ni wallahi ban san wannan hali, ina Abban naku nagan ki ke kaÉ—ai?.

Ni da Yayane bada Abba ba,Yaya bai gaya miki mun kwanta asbiti ba, yanzun haka Abba na shi baa sallame shi ba. Gwalalo ido  Ummie tayi cike da mamaki, ranta lokaci guda ran Ummy ya É“aci, or dama Maman abokin nashi da ba ta da lafiya yake amsan abinci yana kaiwa,ashe Abba ne da Jiddah. Mi ya sameki keda Ibrahim É—in? Nan ta kwashe ciwon Abba tun daga randa suka koma bikin Aliyu ta gaya mata,da kalan azaban da tasha, da sanadin kwantawan ta asbiti, ta gaya mata batasan yanda Aliyu yasan Abba baida lafiya ba har ya kawo shi asbiti,amma yanzun jikin sa alhamdulillah. Ummy tun kafin ta gama ta fara sharan Æ™walla, lallai bata kyauta ba, ta yada zumun ci, da Abdullahi na raye da bata kwashe shekarun nan ba bataje ba nan lafani ga baki ga hanci ko motor haya zata hau É—ari shidda ne, balle ga motocin gidan birjit sai wanda ta zaÉ“a zata hau.








Share ƙwalla tayi kafin cikin da sha shiyar murya tace,"ina Aliyun ya tsaya. Yana waje yace," zai shigo",ta bata ansa a taƙaice. Aliyu ko yana jikin ƙofa yanajin komai dake wakana,ya turo ƙofar ahankali ya shigo, jikin sa a sanyaye, ko kafin ya ƙaraso tsakiyan pallow Ummy ta ture Cute dake kwance ajikin ta ta rai ɓace tayo kansa, yana dago fuska yaji saukan mari tas tas ke ratsa pallow hagu da dama take marin sa. Jikin Cute na rawa ta ƙara haye wa cikin lallausan kujeran pallow ta tura kanta saƙon kujeran a firgie JIDDA ta miƙe tana zaro ido.

Bata tada gani an doke babba ba a Æ™auyen su, gani take in yaro ya girma ya wuce duka, koda ko wani irin laifi  yayi, haka take ganin yayan kauyen su suyi ta ma iyayen su raini amma ba  mai  dukan su, ashe ba haka abin yake ba. Iyah dake hada masu Ummy breakfast da sauri ta aje ta fito pallow tana fadin subuhanallah, lafiya wa ake ma. Turus tayi ta hadiye maganan dake fitowa daga bakin ta ganin Ali zaki ake mari. kasa yayi da kan sa, gaban sa na tsanan ta fadi yana jira kawai tasamu bulala ta fara dukan shi,inde haka zaisa ta huce daga fushin da hau, don ko bijire mata da yayi akan auran Abeeda da wasiyar mahaifin shi da yayi batayi fushi haka ba,ta kauda komi don ta faranta masa ya rabbbb sa'iduni ya furta a zuciyar shi.

Aliyu, ni kake rainawa,ka dauke ni ako da yaushe ba abakin komi ba, banda mahimmanci awajan ka ko,tou wallahi Aliyu ko ban maka baki ba, duniya zata gaya ma, akoda yaushe ba burin ka ka faranta min ba, saide ka É“ata min ko, nagode Allag yasaka maka da alkhairi Allah yama albarka, Allah yabaka abinda kake nema duniya da lahira. Cikin mummunan bacin ran da bai taba sani zata iya ba take maganan, tana kai Æ™arshe batare da tabi takan  kowa ba dake pallow ta wuce hanyar birthroom din ta.

Daga Iyah har JIDDA suna tsaye cirko cirko, JIDDA cike take da dana sanin da bata gaya ma Ummy ba da tasan ranta zai baci har ta mare shi ta gaya munanan kalamai akan shi. Iyah ko mamaki  take mai Aliyu yayi haka da haryasa Hajiya tayi wannan mugun fushin akan sa. Cute ko tana makure waje daya jikin ta har rawa yakeyi. Jidda jiki a sanyaye ta Æ™arasa inda yake tsaye dafe da kumatuka da sukayi  ja ta duÆ™a ta ruÆ™o guywowin sa,wani abu yaji ya ziyar ce shi mai kama da shocking din  wutan lantar ki da  sauri ya ja baya kirjin sa na tsanan ta bugu. Jikin ta sanyi yayi ahankali ta  ta buÉ—e baki tace........!



Post a Comment

0 Comments