f Dalilinda Nakashe Kaina - Sadiya Shehu Lawan

Dalilinda Nakashe Kaina - Sadiya Shehu Lawan



Sadiya Tasha Guba Na Maganin Sauro Dan Baban Ya Baiwa Mahaifiyarta Takarda.....


Budurwar ta rasu ne bayan da ta kwankwadi madarar fiya-fiya da aka ajiye a bayan kofan daki mahaifiyarta don kashe kwari.

A lokacin da muka he yin ta ziyar ita marigayyiyar a gidan su yarinyar a Unguwar Tudun Murtala, mutane suna shiga gidan don jajenta wa iyalan marigayiyar.

Malam Shehu Lawan shi ne mahaifin marigayiyar Sadiya ya ce marigayiyar ta kashe kanta ne a kan ‘matsala’ da ta auku tsakaninsa da mahaifiyarta wadda kuma daga baya suka suka sasanta matsalar.

Ina da matsala da mahaifiyarta wanda hakan ya jawo ba ta yi farin ciki da lamarin, domin ta yi ta kuka a kan hakan daga baya na gaya mata cewa abin ya wuce. Da sassafe na tashi na fita na bar Sadiya tana wanke wanke da sauran yan uwanta lafiya. Ni dai ina kasuwa sai aka yi mini waya cewa an kai ta asibiti. Likitoci sun yi iyakar kokarnsu amma da yake Allah Ya kaddara sai ga shi ta riga mu gidan gaskiya,” inji shi baban Sadya.






Da kungiyar ta tambaye shi ko an yi wa Sadiya miji, mahaifimta ya bayyana cewa tana da manemi “Domin lokaci na karshe da na yi magana da shi ya yi alkawarin zai turo magabatansa da zarar mahaifinsa ya dawo daga Saudiyya don su zo a yanke maganar aure. Sai dai da yake kaddara ta riga tafaru Allah yace auren ba zai yiwu ba, saboda amaryar ta tafi. Ya zama dole in bayyana cewa duk cikin ’ya’yana babu wacce nake kauna kamar Mama sadya. Sai dai a matsayina na Musulmi na dauki wannan lamari a matsyain kaddara ne daga Allah Ina yi mata addu’ar Alah Ya sa Aljanar Firdausi ce makomarta,” inji shi ma aifinta.

Mahaifiyar marigayiyar Malama Amina Shehu ta shaida wa masu rahoto cewa fada ne ya faru tsakanin wata yarinya mai suna Maryam wadda ’yar mijinta ne, sai ya samu kanin marigayiyar ya yi masa dukan tsiya. “Bayan Maryam ta shigo sai ta fara fada da dana Daddy cewa ya yi mata zagin cin mutunci. Lokacin da babansa ya fito daga ban-daki sai ya fara dukan yaron ba ji-ba-gani. Hakan ya sa na kasa hakuri na nuna wa mijina cewa horon da ya yi wa yaron ya yi yawa koda da gaske ne ya yi laifin da ake zargin ya yi wa yarinyar. Sai mijina ya umarce ni da in yi shiru ni kuma na gaya masa cewa ba zan iya ba. Domin ko zagin da aka ce ya yi wa yarinyar a wurin ’yan uwansa ya koya,” inji ita Mahaifiyar ta kara da cewa daga wannan magana sai mijin nata ya yi fushi har ya furta cewa ya sake ta a gaban marigayiyar. “Lokacin da ya gaya mini cewa in tafi ya sake ni sai marigayiyar ta durkusa ta roke shi cewa kada ya kore ni saboda za su shiga wani hali idan na tafi.

Washegari da nake hada kayana na kula marigayiyar tana cikin halin damuwa. A lokacin da nake gaya mata cewa in har don wannan matsala ce kada ta damu kanta domin ni ta bangarena ma magana ta riga ta wuce. Amma abin takaici sai ga shi ta tafi daki ta dauki fiya-fiya ta sha ta mutu,” inji ta.








Post a Comment

0 Comments