f Ashe Kaine Mijina 22 to 31

Ashe Kaine Mijina 22 to 31


Ashe Kaine Mijina 22 to 31


      ASHE KAINE MIJINA


ASHE KAINE MIJINA - 22

ya bude min nashiga, ina shiga motar ban kara sanin inda nakeba, suma nayimi nayi Allah masani, sai farkawa nayi na ganni a wani makeken gado an saka min ruwa, na bude ido a hankali, na jujjuyasu bansan inane nan ba, nayikokarin tashi amma nakasa tashi kaina yayi nauyi, naduba sai naga ashe ruwa ake qaramin, iya tunanina gidan su sister khadee ne tunda daga chan nafito, my be faduwa nayi aka maidani chan.

Kawai sai na daure fuska dan kuwa banason ganinsu. Banason taimakonsu, banason duk wani abu daya shafesu, ina kwance sai ga wani saurayi gajere fari ya shigo, ina ganinsa, na fara surutai, miyasa kuka maidani gidanku, miya dameku da lafiyata da ciwona, Kuma idani gaidanmu banason ganinku ko kadan, haka nayita surutai ina kokarin cire drop dinda aka sakamin sai naji ya rike hannuna, na daga ido na kalleshi baice min komai ba saima bina da ido da yayi ina balaee na, naso in ci gaba sai kuma na fasa sabida kaina yayi nauyi Sosai ihun da nayi, namaida  kaina, na rufe idona, bacci mai nauyi ya kara daukeni banfarka ba sai tsakiyar dare, abin mamaki....?

ASHE KAINE MIJINA - 23

Abin mamaki gajerin katon da na gani dazu shine na gani kwance a gefena yana sharar bacci abinshi, dayake kadon katone Sosai, kuSan gadon ya cika dakin, har yasa ko gurin sallah babu, na tashi ina dube dube ga dukkan alamanan dakin mazane, amma sister khade ta cuceni maimakon ta kaini dakinta sai ta ijiyeni anan? Dakin uncle dinta Wallahi nida ita har abada ta zubar min da mutunci yanzu idan yaya da inna suka ji na kwana daki daya da kato mi zasu kalleni.

Na kare tunane tunane da bala'eena cikin zuciya, nayi niyyar in tayar dashi ya kaini gida amma kuma na fasa, na dago kaina na hango kofa biyu naje a hankali na murda daya najita gam a kulle na murda ta gefenta sai ta budena leqa sai naga ashe toilet ne, ko nayi wanka banida tufafin sakawa gwanda in hakura nayi fitsari nafito, raina duk a bace, ina dubawa naga ledar DAY TO DAY, kuma ledar ta clothes ce sai na buda ina dubawa naga tufafi da brush da duk abin bukatar mace hadda pad ko sista khadee dan uban tace mishi bana sallah ohon mata.










Na dauki ledar na shiga bayi na kulle nayi wanka da yake kaina adaure yake, amma dai gashina anyi sama dashi hakan ya bani damar wanke gashina tsab,nayi wanka kamar ban taba wankaba, ga ruwan da zafi Sosai, duk sanyi da kasalar da suka rage naji sun tafi, nayi brush, amma yunwa ta addabeni, na saka kayan top ne da jeans, nafito kamar baniba, amma zuciyata cike da haushin su sista khadee, ina fitowa naji ana kiran sallah, na tuna inna tace kada inkai maqreeb.....?

ASHE KAINE MIJINA - 24

Kada inkai magareeb, naje na tayarda wannan gajeren yana wani mutsuke ido, mallam ka tashi kaje ka kira sista khade akaini gidan mu ko a budemin kofa inje gida, na fada cike da kadara, wani kallo yakemin, kallon baisan alkiblar maganataba, kallon mi kike nufi, ya tashi zaune, amma kya bari gari ya waye sannan akaiki gida ko, wane gari zan bari ya waye? Yace Bakiji ana sallar asuba bane? Asuba!?? Dama asubace ba maqreeb ba? Kuka ya kubucemini ba tare da nasaniba, miyasa sister khadee tamun hakane? Miyasazata bari ihar in kwana gidansu kuma ta ijiyeni a dakin uncle dinta.

Lallai khadija ba kawar kirki bace, wannan duk araina nakeyi, na dago na kalli mutumin nan, na rasa irin rashin kunyar da zan surfa mai, kawai, nace uncle to sista khadee ta gayawa inna da yaya ina gidansune? sabida inna tace kada in kai magareeb gashi har gari ya kusa wayewa? Yayi kasake yana kallona, kayi magana mana uncle, yaji dadin sunan data kirashi dashi, har yana maimaitawa a fili uncle, amma kuma shi wacce sister khadee ce takefada haka, Lallai idan yagaya mata baisan sister khadee ba wannan rudaddiyar zata daga mishi hankali fiye da na yanzu, amma zai lallabata har gari ya waye sai ya mata bayanin komai, da sanyin murya yace ki zauna in miki bayani, kinji sister na, da jajayen idona na dago na kalleshi jin ya fadi sunan da yaya yake kirana dashi, sai na sami kaina ina maibin umurninsa, nazauna girmn kai ba nawa bane nan.....?

ASHE KAINE MIJINA - 25

Na zauna, kiyi hakuri zuwa wayewar gari zan gaya miki komai, kinji? na daga kai alamar shikenan ba komai, na zauna jigun, chan natuna banyi sallar koazzahar bare magareeb gashi har an kira asuba, na mike naje na dauro alwala nazo nayi sallolin da suka hau kaina bayan na kammala nayi sallar asuba nayi addu'a Allah ya fitar dani wannan qangi da sister khadee ta jefani, yatsareni da sharrin uncle dinta.

Anan zaune bacci yayi awon gaba dani ban farkaba sai guraren tara na safe,ina farkawa na duba bashi ba labarinshi, na tashi na murda kofa najita kulle gam, ga boyfriend nan an hadamini an ijiye mini, wasu zafafan hawaye suka gangaro a kumatuna Lallai sista khadija ta cika yar iska! Wato haka zata min ko? 

Ba wata mafita illa in danne abincina in barwa Allah ko na mutu in tafi ciki da nauyi.

A bangaren iyayen nazia kuwa tunda inna taga an kira magareeb bata dawo ba ta kira wayar nazia, tana ringing amma ba'adauka, tayi ta kira har ta kufulata daina kira ta dauki alwashin idan ta dawo zata gane kurenta, shiru nazia har karfe goma bata dawoba, sai hankalin inna ya fara tashi, ta dauki waya kena zata kira yaya hafeez sai gashi yazo, kasan fa har yanzu nazia batadawo ba, haba dai,? Allah kuwa! Kuma nayita kiranta bansametaba, to baki kira kawar tataba? Yes ban kiraba, to bari in kirata.









Saida ya kira sau uku ana hudu aka daga, batayi maganaba shi ya fara sallama aka amsa mishi sama sama, yanzu inna take gayam nazia har yanzu batadawoba! Kuma tace gidan ku zataje kamar yanda kika roka na amince ta tafi, tace Nazia kuma? Ai batazo nan ba, What! ......?

ASHE KAINE MIJINA - 26

What, yes batazo ba nace, ai kuwa tun safee tafito gida tace zatazo gidanku, kamar yanda kika bukata inna ta barta tazo, hmmm to kuwa banan tazoba, sai ku kira wayarta kuji ina yarku take. Ban yaji ta katse waya bata ma saurari abinda zai ce mataba, ya juyo yayiwa inna bayanin abinda khadija ta fada hankalinsu duk ya tashi, suka fito aka fara chigiya unguwa unguwa har kofar rini unguwar su sista khadija saida akaje nemanta, ammabata ba labarinta, gashi dare yayi, haka suka kwana zaune, ga wayarta na ringing amma ba'adauka guraren asuba ma wayar sister daina ringing hankali ya kara tashi, tunda asuba yaya ya koma police station aka kai hotonta ana  cigiyarta, aka kai gidan tv gidan radio jarida duk aka baza ana nemanta, amma har guraren 12 na rana ba ko karenda yace ya ganta, Tana zaune ta tanqware gafafu, taji ana murda kofa, tuni ta mike tsaye tana jiran shigowarsa, yana kunno kai dakin da sallamarsa da murmushin sister har kin, sai saukar mari yaji a fuskarshi, kai mahaukacin inane da zaku kawo gidan maza ku ijiye, idan ita khadija yar iska ce to ni ba yar ita bace kuma ka gaggauta maidani gidn mu, ya dago da sauri ya kalleta, ya daga hannu zai mareta kome ya tuna kawai ya sauke hannunsa,ya dunkule hannurai bace ya mata wani kallo ya wurga ledar da ya shigo da ita ya ja kofa ya kulle ya tafi abinshi, sai tafara dana sanin hukuncin da ta mishi, tafara.

Allah wadai da zuciyarta,da kuma rashin kunya irin tata, miyasa ta mishi haka. Lallai bata kyauta ba gashi ya tafi ya barta,jiya ta mare shi yauma ta mare Shi, itako haka xata kare da dukan maza, keke idonta ba kuka ba alamunsu ta mike ta janyo ledar Abincine take away guda biyu komai dai guda biyu, da alama da nashi da nata dasu drink da ice cream duk a ciki, ta bude ta sa abincin gaba amma ta kasa chi tayi tagumi ta tashi tayi sallah azzahar tananan zaune har la'asar tayi sallah taga cikinta ya fara ihu, ta janyo abincin taci ta koshi,a haka bacci yayi awon gaba da ita....?

ASHE KAINE MIJINA - 27

Gaba da ita har dare yayi bashi ba labarinsa guraren sha biyu ta dauko abincin dazu, dayan da ya rage ta chinye, shiru shiru har bacci ya dauketa bata farka ba sai guraren biyar, bashi ba labarinsa, amma kuma ya ijiye mata ledar boyfriend.







Hakadai wasa wasa har saida Nazia tayi kwana hudu a gidannan bata kara ganin saba, kuma kamar aljani sai tayi bacci yake kawo mata abinci abin yana daure mata kai, yau ta dauki alwashin bata ba barci, har kusan magareeb ba'a kawo mata abinci ba, data gaji da jira sai ta dan gyangyada baccin da tashinta duka minti hudune amma har ya kawo abinci ya fice abnshi, tunani kala kala takeyi, ta fara tunanin ko ta daina cin abinci ne, wata zuciyar tace ki danne abinki ko kin mutu kije da nauyi.

Duk tayi wani iri da ita ammafa bata rameba ko kadan dan kuwa bata wasa da abinci saidai akwai alamar tashin hankali tare da ita, Iyaye anyi sanarwa har an gaji bata ba labarinta, anje gun malamai suna ta addu'a anata sauke qur'an Allah ya bayyanata amma shiru sister khadija kuwa bata ma san cewa har yanzu ba'aga nazia ba, hankalinta kwance tana al amarrunta, ko a skull da andauko zancenta sai tabar gurin batason zancen, bata San zancen batanta akeyiba, su kuma sauran sun dauka haushin rashin kawane yakesa bata zama cikin mutane musamman da ake cewa garin zuwa gidansu ta bata.

Yaudai bazanyi bacci ba sai naga aljanin da ke ijiyemin abinci, baccin kariya nayi ya dauka nayi bacci ko minti uku ba'ayiba naji ana buda kofa a hankali bayan ya bude sai kuma ya tsaya kamar bayan minti daya sai aka turo kofa ina jin ya turo kofa nayi zubur na miqe dama akan dadduma nayi baccin gefen kofane.....?

ASHE KAINE MIJINA - 28

Kofane, yana Shigowa na mikke dan Allah uncle kayi hakuri, da abinda namaka dan Allah ka kaini gida, aranshi yace dama batayi bacci ba.

Ya tsaya bakin kofa ya toge, ina tsoron in shigo ki mareni! Ko ki dakeni dan nakula bakida lafiya!! Naji zafin maganar amma na Shanye yaci gaba idanhaukar taki bazata motsaba in shigo, kuuuuut dan na mareShi zaicemin mahau kaciya, na dako na kalle shi namai kallon raini har na hada bakar maganar da zan yaba mai, kawai na sunkuyar dakai kayi hakuri uncle.

Yashigo dakin ya zauna, ya kalleta ashe ganin da yake mata a camera ba haka bane duk ta firgice a camera kuwa yana ganinta kaman lafiya lau,Yana zama ta fara jero mai tambaya.









Miyasa ka ijiye ni anan? Mi kakeso in maka?Baka tsoron Allah ne? Ko kai ba musulmi bane? Baka tananin halinda iyayena zasu shiga? Is ok? ya katseta, da daga mata hannu kansa na kallon kefe, ta dago ta kalleshi, ki natsu kiji mi zan gayamiki!! Na farko Idan na fara magana kada kiyi magana sai na kare, kinajina? Yes naji! Ya juyo ya kalleta tausayinta da yanda ta bashi amsa ya kamashi , lokaci daya sonta da sha'awar kusantarta ya kamashi, ya hade yawun dole, gashi ta wani mishikyau, tufafin sa ne a jikinta top da wando, yayi sauri ya kawar da kai, ya mike tsaye idan har yakuSan ceta bai mata adalciba, dan kuwa yayi niyar keta mata mutunci ladar mari da ta mishi amma kuma tausayinta ya rinjaye shi, ya mike anjima zan miki bayani, zatayi magana, mi nace miki.

Ta tuna yace kada tayi magana, ta kalleshi taga idonsa taga ya kada yayi jaa, sai taji tsoro, ya fita, mamaki ya kamata yanda ya sauya lokaci daya, taci abincin tayi sallar tana nan za une sai gashi ya shigo, abin mamaki bai kalli ko gefenta ya zaune ya juya mata baya....?

ASHE KAINE MIJINA - 29

Ya juya mata baya, yafara da cewa ranar assabar na dawo daga kasuwa sai naga kamar kina neman taxi, sai na tsaya in rage miki hanya dan unguwar nasan ba'acika samun taxi ba, abinda ya bani mamaki yanda idonki ya rufe kika kasa banbance motana da taxi, dan ni ba dan taxi bane,har kina gayamin address dinki, bawai nagane bane nayi niyyar idan naje unguwar naku sai ki nuna mini guri in saukeki, bayan mun isa unguwarku na miki magana nace mun kawo naji shiru ina ta magana kikayi shiru nadauka gyaleni kikayi nayi magana har na gaji sai kawai najuya kan motana na wuce gida nakai sakon baba.

Mun kama hanyar gidana in dauko wani abu bayan na iso nan sai na kara miki magana shiru,ba motsi na tabaki naji bakya nunfashi, hankakina ya tashi matuqa, tsoro da fargabar idan kin mutu ya zanyi dake ya kamani, a haka na daukokoki na kawo ki dakina batare da na bari kowa ya ganki ba, dama ni Dr ne, na miki treatment, na kara miki ruwa har zuwa lokacin da kika farfado kika fara zagina,to kinji atakaice yanda akayi na samoki, ni banida alaka da wata sister khadija hasalima ko sunan ban tabajiba, kuma zan gaya miki Gaskiyar magana sonki nakeyi,taji wani dummm aranta tace idan dai zaka kaini gida mai sauki ne, ya kara mata mata bayanin lahinda ya sami kanshi dazu na ganinta da yayi, kuma ya nuna mata cameran da yake ganinta idan zai kawo mata abinci dan bayason ganinta, tun ranar da ta mareshi kuma yayi alkawarin horata har na kwana bakwai yama yi nufin keta mata mutunchi Allahne ya kareta sai kuma Allah ya taimaketa, nan itama tabashi hakuri rashin kunyar da ta mar da taimakon da ya mata, takuma hadamai da labarin abinda ya faru daga farko har karshe, yayi mamakin irin zuciyanta da kuma yanda take iya dukan namiji, yaga marin da tayiwa unlce din sister khadija ne ya janyo mata haka, dadewar da tayi anan ma sanadin marin da ta mishine, yanzu dai kisharya inkaiki gurin inna...?

ASHE KAINE MIJINA -  30

Ki shirya inkaiki gurin inna, wani sanyi naji araina,nayi tsalle da ihu, inata dariya murna, "nima jabo na matsu inga yanda zata kaya gaba",tace ai ashirye nake, ya juyo ya kalleni karo na farko daya kalleni tunda ya shigo dakinnan, kin cire mini tufafina? Yes yanzu zan cire, shine kike cewa kin sharya? Murmushin da tayi ya kara daga mishi hankali, yasa kai idan kin shirya ina waje ki fito muje, yana fita na cire kayanshi na maida wayanda ya siyomin koda sunyi datti amma su na saka hakanan nafito na sameshi, abin mamaki gidan da nake qaton kaskene kuma part part ne ga mutane a ciki suna kai da kawo, a raina nace dana sani da na rika dukan qofa tun Lokacin ai da za'a jiyoni a bude min da yanzu na tsufa gida.










Mun isa unguwar mu da misalin qarfe tara na yamma, na rangada sallama inna tana ganina ta fara salati Sai kawai ta fashe da kuka nima na fashe da kuka, tana kuka ina inayi tayi wa yaya waya ko minti biyar ba'ayiba ya iso, yana zuwa naje na rungumeshi ina kuka, araina nace ni ban rameba su suka rame, duk sai suka qara bani tausayi, nan aka fara tambayar ya akayi? Na koro musu bayani daga farko har karshe, sun tausayamin kuma mamaki ya kama su, suka gayamin rashin mutuncin da sister khadee ta musu, anan dai wanda ya kawoni shima yayi bayani nashi, sai dai yayi karya sabida ce musu yayi sai jiya da dare na farfado kuma yace tsoro yaji ganin lalacewar kasa kada yakaini gurin yan sanda ya janyo wa kanshi wani abin daban, to hakadai a ka jajantawa juna akayi waya kauye aka sanar dasu an ganni iyayen nura sunji dadi Sosai inna tace gobe sai ayi sadaka....?

ASHE KAINE MIJINA - 31

Sai ayi sadaka tunda Allah ya mayar dani gida, yaya sai kallona yakeyi kamar wata bakuwa na tashi naje na haye shi ina dariya sai naga uncle habeeb ya daure fuska na rasa dalili,anyi hira sosai inna tana bada labarin yandayaya yayi shima yana bada labarin yanda tayi cikana kamar ya kulle dan dariya," nima jabo na dara, "munchi mun koshi yaya yace sai na warware zan koma makaranta uncle habeeb dai ya kara gaba abinshi ya karbi number yayi data inna.


Yaya ya Siyo min siyomin sabuwar wayah da sabon sim, sabon gata da kulawa wajen inna da yaya ba'a magana, kusan kullum sai unle habeeb yazo gidan mu har dai ya shaqu da inna ya zama kamar dan gida tun da inna ta fahimci sona yakeyi kamin ma ya furta take bashi labarin nura kuma ta gaya mishi Lallai wasiyar mahaifinane in auri nura, baiji dadin rasani da yayibahakan kuma baisa mun daina zumunci dashiba, amma ya rasa wani farin cikin sa, yan gidan su sun sammu muma munsansu har zumunci mukeyi.

Saida nayi wata biyu chur a gida sannan aka fara maganar komawata makaranta, yaya habeeb yace a chanzamin skull, haka kuwa akayi aka chanza skull, ban kara jin labarin sister khadee ba, Ranan munje bakin auren kanwar uncle habeeb nida inna muna dawowa a hanya mota tayi tsayinta na kunna na kunna taki tashi munanan tsaye saiga wasu Guys sun wuce sai inna ta musu hannu har sun wuce Sosai sai suka dawo, da yake ina cikin motar ne, ki fito ga wasu yan samari nan na tsayar kinsanba jin maganata zasuyiba, nafito suna zuwa suka fito motar su, sai dayan guys din yace kace kamar kasan matar kuma kace tsohuwace, yes Wallahi kafa San yau tin safe nakejin faduwar gaba, kirjina sai dukan uku, uku yakeyi i don't know you. Yanzu ma Sai naji ya karu, ita tsohuwar fa, Share Ashe ba tsohuwa bace manyan kayace, suka kwashe da dariya, suna kokarin tsallakowa, amma fa daga farko tsohowar dana gani kamar na santa amma na manta inda nasan ta, any how tunda munzo mutaimaka musu kawai, inna dama tana ganin sun dawo ta ta shige mota abinta, abokin deen ya shiga motar yayi danne danne sai kawai motar ta tashi, tunda suka zo naji jikina ya chanza na Kasa dago kai in kalle gefen da nakejin ana kallona, muje ko deen dayan abokin ya fada amma ina deen yayi Nisa, Na dago da kyar na kalle mai maganar nayi godiya zan zaga yace idan ba damuwa ki bamu number ki, murna kamar ta kashe deen, Lallai yayi dacen aboki da yake gane duk wata matsalatashi, na bashi number bada son raina ba dan kawai mutunchin da suka mana ne....?

contact-form

Post a Comment

0 Comments