f Ashe Kaine Mijina 32 to 44

Ashe Kaine Mijina 32 to 44

 

Ashe Kaine Mijina 32 to 44


    ASHE KAINE MIJINA


ASHE KAINE MIJINA - 32

Har ya juya zai tafi sai yaga bari dai yayi ta maza yaji sunanta, yes, am, inn, duk ya dabirce, dagyar ya iya furta kalma biyu M deen by name, what of you please?

Na kalleshi a raina nace wannan kamar wani gaula daga kallon mutane kuma sai Kasa magana. Nace bari in fada mar Sunan da inna tace babana yana kirana dashi, M hulwah, wawoo nice name, yamin wani murmushi bansan dalilin da yasa naji rass ba, nima na maida mai, owk hulwatiy sai kinjimu, yana murmushi yana sosa qeya kamar mara gaskiya, suka wuce nashiga mota inna tace da ace sun ganni ko taimakon ma bazasuyiba, na kyalkyale da daria wallahi inna akwi ki da zance akanme bazasu taimakamikiba? To Sunga tsohuwa.










Haka mukayi ta hira har muka isa gida, muna isa naji sako a WhatsApp, na duba naga sabuwar number kawai sai nayi blocking din number, dan Banason shirme, kuma nasan ban bama kowa number naba, sam na manta da na hadu da wani wai shi deen har na bashi number, sai da dare na kwanta bacci amma ina bacci yaki zuwa, sai juyi nake, karo na farko a tarihin rayuwata da na taba tsayawa tunanin Wani namiji, sai karan to fuskarshi nake,murmushin da ya mun yake min gizo bacci yau kaura cemin, a raina nace wallahi guy din ya hadu sosai, Nasami kaina da kara yin murmushi na janwo pillow na matse gamm, lokaci daya na tuna an mini magana ta WhatsApp my be ma shine nayi blocking dinsa ai kuwa dana chuchi kaina, na je neman phone din, na janyo ta qasan dadduma naga 8 miss call, natabbatarda cewa shine, yayo sms hudu, na budeshi, Na duba number sai naga d Same number da aka kirani da ita aka mun magana ta WhatsApp akamin sms, na bude nace salam, Kamar yana jira dama, ya fara surutuai. Haba hulwaty, ya zan kiraki kiki dauka kinsan kuwa abinda nakeji araina....?

ASHE KAINE MIJINA - 33

Araina kuwa? To? Let me call you, No ka barshi let us chat, Why my hulwah? Dalilinda yasa, dare yayi yanzu! Owk hulwaty, Hakadai yayi ta yimin kalaman soyayyah masu kashe jiki, duk abinda yaake fadar yana feeling nima ina feeling dinsa but ni na barwa chikinane dan banga amfanin yin haka ba tamkar na bada kainane ranar farko, sai hmmm, da owk da lol nake tura mishi, bai barni barni nayi bacci ba sai qarfe ukuna dare ni kaina bansan lokacin yayiba, kuma banji bacciba, zan iya cewanafada tarkon son deen, koda nasan cewa ni matar wani ce, abinda ya hanani kula samari kenan a rayuwata, amma wannan karon an sami akasi sabida dare daya deen ya sacemin zuciya, sonshi ya kamani,wanda nima jabo na hango hakan a fuskar nazoon inna. 

Wasa wasa har na kare secondary skull, wanda yayi daidai da cikata shekara 18 kuma shekarar mu biyu tare da deen muna barza soyayyah dashi, amma ba wanda yasani a gidanmu, duk soyayyar da muke a waya mukeyinta ko kuma idan naje Shopping mu hadu mu hadu, amma ban taba gigin kawoshi gidan muba, dan nasan zanci ubanane gurin inna, yayi korafi har ya gaji, amma ba abinda ya chanza, har cewa yake bana sonsa amma haka nake shanyewa. Inaga ba wata halitta da ta tabason juna kamar yanda nida deen mukeson junan mu, kuma ayanda na fahimta deen dan duniya ne na qarke, yanason rayuwar duniya amma haduwar mu dashi komai yasha banban so dayawa abokinsa yakance dani, nayi jihadin da ko mallam yakasa yin irinsa.

ASHE KAINE MIJINA - 34

Yakasa yin irinsa, na maida deen mutum, kamilalle nima na kula da haka, sabida deen yadaina wasu saka tufafi na mahaukata waishi swagger, wani Aski, duk ya daina, rashin kunya da Wulakanta mutane duk ya ijiye su ya natsu Sosai, nima naji dadin haka.

Wai, inna, yau Allah ya rabani da tashin asuba zuwa skull, na girma yanzu.








Inna tayi dariya, ina fa ya rabaki dashi tunda idan kinyi aure dole ki tashi kiyiwa mijinki girki, kamin yaje aiki.

Kamar ta dakamin guduma a kirji, na fuske inna ana aure ba miji.

Ba'ayi kam, to kingani ai sai na sami miji sannan zanyi aureko inna, inna tace nuran fa. Haba inna nura sona yakeyi, nura damuwa yayi dani, Kiduba fa shekaranmu uku hudu a garinnan bai taba kiranaba kuma kin tanbbatar da yana garinnan,hatta kauye idan yaje baya zuwa guna, sai kace mara gata haka za'bashi ni kamar abar sadaka, ki kalla fa hadda ko batan da nayisau daya yayi miki jaje, shima bayan Sati uku sannan ya kira, da ya damu dani da yazo ya dubani amma shiru ni gaskiya inna yanzu an daina wannan kauyanci auren hadi, auren kauye, nasan da ace baba yananan koshi bazai bari in aureshiba wallahi, yanzu fa ki duba inna ace t, ke rufemin baki da shegen iyayin tsiyaa, ni zaki nunawa boko, wayewa taci ubanta! Wallahi ko kinqi ko kinso, sai kin auri nura, sabida marigayi yana cikin halin mutuwa saida ya jaddadamin kada in kuskura in raba aurennan matukar ba shi nuran yace ya janyeba, to wallahi in gaya miki kinyi kadan kisa akalleni mutuniyar banzaba....?

ASHE KAINE MIJINA - 35

Banzaba gara ki rufawa kanki asiri ya fiye miki, dan ba chanza wannan zancen za'ayiba, na mike traye ni wallahi inna banasonsa, de Tas naji saukar mari kamin in bude idoin dawo hayyacina tuni inna ta mike tsaye taci gaba da masifa,tunda nake ban taba ganin inna na rigima ba sai yau, ashe inna ma idan tayi fishi tana ja kamar dai yaya.

Wato shi yasa kikace sai kinje " university" to ba inda zaki boko ya mare, a ure za'amiki cikin watannan, naga karshen fitsara ta wuce ta barni danne da kumatu ina kuka.

Tabdijan, nifa a tunanina mutuwace kawai zata iya rabani da deen dina amma gashi lokaci daya, inna na neman ta tarwatsamin farin cikina, tana neman ta jefani cikin kunci da bakin ciki da zullumi,! Wallahi da in rasa deen gwanda in rasa rayuwata, sabida shine rayuwata, ni kaina bansan irin sonda nake masaba sai yanzu, sabida yanzune nakejin wata azaba araina, naji na shiga kunci, da damuwa!, inaji ina gani za'arabani da deen wallahi bazan yardaba, sam! Yaya yazo nakai kukana gareshi, dama shi yaya bayason nura sabida ya kula basona yakeba, amma ba abinda zaiyi illa ya bani hakuri in bi umurnin mahaifana ni nazia ina zan saka kaina, na tashi sumai sumai na wuce daki naci gaba da kuka na....?

ASHE KAINE MIJINA - 36

Na wuce daki na kulle kaina ciki, na dauki waya na kira deen dina, ringing daya ya dauka, hello my hulwah.! Bansan Lokacin da wasu zafafan hawaye suka kankarominva, tabbas saidai akasheni bazan iya rabuwa da deen ba, bazan iya rayuwa idan bashiba.

Hulwaty kinyi shiru, na kasa magana sai na kashe wayar ya kira sau uku a na hudu na daga, ina dauka na rushe masa dasabon kuka hankalinsa idan yayi dubu saida ya tashi na gaya masa aure za'amin a wannan watan, kukana ya karu, yayi shiru, chan yafara magana muryarshi na rawa tana sassarkewa, damaa nasan ba sona kikeba, dama nasan yaudarata kike! Shi yasa kikaki nunamin hatta gidanku, tuntuni kinsan anmiki miji miyasa kika koyamin kaunarki? Miyasa kika bari na shaku dake? Miyasa kika bari saida nakai haka sannan zaki gaya min cewa an miki miji? Kinsan kina da wanda zaki aura miyasa kika shigo rayuwata.









Kin cuceni hulwa! Zaki azabtar da zuciyar da ta mutu akanki! Wallahi tallahi bazan juri ganinki tare dawaniba a matsayin mijinki, idan kuwa har hakan ta kasance ina mai tabbatar miki zan iya rasa rayuwata! Baibarni nace komai ba ya kashe wayar, nayi kira har na gaji yaki dagawa karshe ya kashe wayar! Tabbas zan shiga tsaka mai wuya, wallahi bazan iya barinka na deen koda zan rasa rayuwata, kaine farin cikina! Kaine rayuwata! Kaine ganina! Wani sabon kuka yaci karfinta, "tabbas hauwa jabo tayi gaskiya da tace so ya mayar da ita makauniya mahaukaciya kurma wawuya, mara bin umurni mara ra'ayin kanta'" sai yanzu nake fahimtar abinda take cewa! Namike a fusace na nufi kofa....?

ASHE KAINE MIJINA - 37

Na nufi kofa bana gani Sosai jiri jiri nake gani dama gani ba auki ba, amma haka na nufi dakin inna, da nakai bakin kofa kuma sai nayi turus, tabbas bazan iya bijirewa mahaifiyataba koda zan rasa raina, kuma bazan iya hakurinrashin deen dina ba! To ina mafita? Babu!

Ba abinda nake tunani illah ranarda za'a daura min auri da wani ba deen dina ba!

Haka na juyo jiki ba kwari na dawo daki naci gaba da kuka, gashi kiran duniya nayiwa wayar deen dina amma a kashe,

Da wanne yakeson inji? Da bakin cikin auren wanda baya sona koda bakin cikin rabuwa dashi.

Haka nayi sati daya a daki banachin komai sai tea, kuma inna ko ta kaina batayiba, ga deen dina wayar shi a kulle, yau da safee ina zaune na hada kai da guiwa, kawai naji karar wayata banyi niyyar dagawaba da naga bakuwar number sai kuma na daure na daga, abokin deen yake shaida min deen ba lafiya yana asibiti yau kwana shida kenan hankalina ya gama tashi, na rarrafa naja mota sai asibiti ina shiga na hadu da tsohuwar kawata sister khadija itada ammar dinta tana mishi iyayi shi kuma yana biye da ita, tamin kallon mamaki, tanamason tamini magana amma ni banyi takantaba,dan hankalina baya tare dani kallo daya na mata na kauda kai Na shiga inda akacemin an kwantarda deen dina, ina zuwa naga ya rame yayi wani iri, na matsa kusa dashi kamar in fada jikinsa in nuna masa sonda nake masa da missing dinsa da nayi amma kuma ba hali, haka na daure nayi tsaye ina kallonsa ina kuka, kamshin turarena ne ya daki hanchin sa hakan. yasa ya bude idonsa yana ganina ya rufe idonsa ya juyan baya, Bashir bashir, yanzu ma Wallahi idan na bude ido ita nake gani, kamshinta nakeji, please ka kawo min hulwaty na.

Yanda yake magana yasa ta fashe da kuka, hakan yasa deen ya bude idonsa a hankali ya tabbatar da ba gizo take mar ba, kuma ya chanza zance miya kawoki gurina....?

ASHE KAINE MIJINA - 38

Miya kawoki gurina? Kinzo ki karasaninie? Ki sani kin cuci rayuwata hulwa! Yana magana da kyar muryarsa na rawa,har ya Kasa magana haka ya saki kuka hihihi kamar karamin yaro, na rufe masa baki da hannu, ina bashi hakuri, duk da cewa nima kukan nake amma kamar nafishi karfin hali, na samuna lallabashi, yayi shiru, na kwantar mishi da hankali da kalamai masu dadi abin mamaki cikin 30mit har ya fara murmurewa a fuska saidai rama kamta nanan a tare dashi, "ni jabo araina nace Lallai taku soyayyar daban ta ke" na dade muna hira har yake bani labarin Nihal dinsa zata tafi karatu canada, koda bansan taba ina yawan jin sunanta a bakinsa, kuma dukkan alamu yanasonta sun shaku sosai, yar yayansa ce, munyi hira Sosai nidashi duk mun sami walwala, kamar bamuba ban koma gidaba sai wajen 4PM nakoma gida, da yake inna ta fita harkata batasan nafitaba batasan nadawoba.











Inna tayi mamakin ganina a pallow yau tun bayan sati daya da suka wuce, har yaya na hira ina dariya, na ga alamar taji dadin haka Sosai amma bata bayyanaba amma ya bayyana a fuskarta, ina zaune muna hira sai ga uncle habeeb yana shigowa ya fara zolayata, amarya kinsha kamshi, raina ya sosu, wani bakin chiki ya tullokoni kamar in mare shi, shima na kula da damu wa afuskar shi, banji dadin sunan ba, sunan baima dace daniba, nayi yake, kinga yanda kika rame kuwa? yaya Habeeb, ai inna tacemin tunda aka miki zancen aure Kika shiga halwa, kullm nazo bana ganinki, dazu yaya hafeez yake cemin angon ma naki yaje gurinsa dan suji yanda za'ayi ashe bashida lafiya zazzabi yakeyi kwana biyu, amma ance yau ya sami sauki, Allah ya kara lafiya, nace ameen araina nace Allah ya kashe dan banza in auri deen dina....?

ASHE KAINE MIJINA - 39

Nace ameen, inna tayi mamakin amin dinda nace, amma bata nunaba, haka mukayi hira Sosai da uncle habeeb ya debemin kewa Sosai.

An saka ranar aurena yau saura sati daya, zainab khalifa ta tare gidanmu tunda aka fara shirye shiryen biki, gaskiya tanada kirki zainb yaya ne kawai ya tsaneta gata yar gayu wayayyiya,duk wannan abin da akeyi zainb da abokin nura takeyin Su, dai dai da rana daya ango bai nemeniba, nima ban nemeshiba.

Gaskiya dangin nura sun nuna gata ta uwa da uba, musamman babban yayanshi da ya rikeshi, sabida komai na aure sun mini na gani na fada duk abinda ake yiwa yar gata an mini, fatima kawata ta kauye tazo, maimakon taje gidan Su Sai ta tare gidan mu da zama, zainab khalifa da fatima su suka rarraba katin gayyata da anko wa kawaye da abokan arziki, amma ni ba hannuna aciki ba wanda yasan abinda ke zuciyata sai Allah, duniya tamini zafi, na rasaa yanda zanyi da rayuwata, Saura kwana biyu a daura aurena, deen dina ya kirani yana kuka wiwi kamar karamin yaro dama shi haka yake San garta tamai YAWA kamar jinjiri bayajin wuyar yin kuka, yana kuka yake gayamin wai za'amishi aure, shima yamin bayanin komai, inaga zafin kishin da naji deen baijishiba, na ci gaba da kukan da yafi na farko aka rasa gane kaina inna tace kar wanda ya ku lani, deen dina yake tambayata ya zamuyi, nace mubi maganar iyayenmu yace shi bazai iya hada jiki da wata idan baniba, duk abinda ya fada nace nima haka? Yakenan?

Qarke dai Munyi alkawarin dagani harshi, ba wanda zai kula wanda aka auramai kuma duk mun amince da hakan, zan kashe aurena kamar bayan wata hudu shi kuma zai saki matar da watahudu dai dai nan sai muyi auren mu, kuma ba wanda zai tuhumeni sabida dama ansan yanda auren yake....?

ASHE KAINE MIJINA - 40

Yanda auren yake, mun amince da hakan haka kuwa akayi, ranar assabar akadaura auren,.

NAZIA & NURADDEEN.

Aurenda ya sami halartar manyan kusoshin gwamnati da manyan yan siyasa da manyan malaman kasar nan duk abokan yayan nura ne da kuma abokan yayana, mutane kamar me, amma abin haushi ba ango ba labarinsa wajen daurin aure, abin yayiwa yayan nura zafi Sosai sai ya bime da cewa ango ya tashiya matsanancin ciwon ciki, kuma an riga an tara mutane shiyasa aka daura auren, yana bama mutane hakuri akan rashin halartar ango.

Ana shagali haka na sulale naje ban kwana da deen dina, a wani gida muka hadu dashi, anan ni kuka shi kuka,ba mai rarrashin wani, kaunar juna ta rufe mana ido zuciyoyin mu sai harbawa suke ya rungumoni, yana shafani yana rarrashina, sam na manta da an daura min aure, koda wannan shine karo na farko dana hada jiki da deen duk kuwa kaunar juna da mukeyi, nida deen kabaki daya mun fita hayyacinmu, nidai ban tabajin abinda nakejiba yanzu sabida shine karo na farko dana kusanci namiji, kuma namijin ma wanda nafi kauna arayuwata, in takaita muku dai deen yayi nasarar kawar da budurcin hulwarsa, duk tsimin da ake dura mata,sai da ya Siga, kundai san sakwatawa da hade hade, wallahi haka deen yayi nasarar kawar mata da budurcinta, tun tana kuka, har ta daina kuka numfashinta ya rika fita sama sama, sabida taji jiki, ga budurci kuma ga magungunan da aka kimsa mata cikin ma wasu idan sun shigo hannunta a shara take zubawa, amma ta hadu hadi, ke in takaita muku saida deen yayi kusan awa daya da rabi akan nazia yana abu daya,Kuma ba wanda ya gaji cikin Su bare yayi kokarin hana daya, ba wanda yana da aure, karar wayarshine ya mayar dasu halinda suke ciki, abu nafarko da yazo mishi shine yayi zina da matar aure? Subahanallahi.

Bayan kowannensu ya dawo hayya cinsa sannan suka fuskanci illar laifinda suka aikata, tabbas basuda uzuri gurin Allah, kuma hukuncinsu dukansu kashine, A bangaren nazia kuwa zuciyarta cike da farin ciki, ganin cewa koda wanchanwawan mijin nata yayi nasara akanta ta biyawa zuciyarta bukatarta, lallai har yanzu akwai yarinta cikin nazia, ita sam bata hango illar laifinda tayiba, amma kuma ta kasa tashi, da gyar tasamu ta mike da taimakon deen tana dingishi, batada time din wanka, haka ya dingisa ta dawo gida, dama bataje da wayaba, har tazo bakin gofa tace bakace kunshina yayi kyauba, yayi murmushin karfin hali yace ai bani aka yiwabako, ranta ya sosu Sosai. 










Batace komai ba ta dingisha ta tafi, gida, bawanda ya gane cewa amarya ta fita an dauka taron jama'ane ya boyeta, ta dawo dab da magareeb zafin saduwar da sukayi ne yake damunta, ta wuce bayi tayi gashi da kyar, tayi wankan tsarki ta, tana bayi taji inna na nemanta, taje ta sameta inna ta mata nasiha mai ratsa jiki, saida tayi kuka, aka shiryata za'akaita gidan mijinta kamin nan aka kaita gidan yayan nura din, duk da cikin kuka take kuma fuskarta a kulle take bai hanata gane gidan ba Gidan su sister khadjida ne tsohuwar kawarta da taso ta salwantar da rayuwarta ita da mugun uncle dinta amma ta ijiye akan cewa my be sun saida gidanne yayan nura ya siya, da yake bata shiga gidan ba, so bata san yanda gidan yake ba bare ta gane, kawai dai an yiwa gidan sabon fentine, sun shiga an mata nasiha maman nura da babasu da yayyenshi da matar yayanshi da duk danginsu suntofa albarkacin bakinsu, ana ta sakamini albaka ana dada cewa inyi hakuri, aka kwasheni sai gidan mijina...

WASA SABON GIRKI, KU BIYO JIKANYAR JABBI YAR MUHAMMAD

 JABO KUSHA LABARI


ASHE KAINE MIJINA - 41

Yanda auren yake, mun amince da hakan haka kuwa akayi, ranar assabar akadaura auren.

NAZIA & NURADDEEN.

Aurenda ya sami halartar manyan qusoshin gwamnati da manyan yan siyasa da manyan malaman kasar nan duk abokan yayan nura ne da kuma abokan yayana, mutane kamar me, amma abin haushi ba ango ba labarinsa wajen daurin aure, abin yayiwa yayan nura zafi Sosai sai ya bike da cewa ango ya tashiya matsanancin ciwon ciki, kuma an riga an tara mutane shiyasa aka daur a auren, yana bama mutane hakuri akan rashin halartar ango.

Ana shagali haka na sulale naje ban kwana da deen dina, a wani gida muka hadu dashi, anan ni kuka shi kuka,ba mai rarrashin wani, kaunar juna ta rufe mana ido zuciyoyin mu sai harbawa suke ya rungumoni, yana shafani yana rarrashina, sam na manta da an daura min aure, koda wannan shine karo na farko dana hada jiki da deen duk kuwa kaunar juna da mukeyi, nida deen kabaki daya mun fitahayyacinmu, nidai ban tabajin abinda nakejiba yanzu sabida shine karo na farko dana kusanci namiji, kuma namijin ma wanda nafi kauna arayuwata, in takaita muku dai deen yayi nasarar kawar da budurcin hulwarsa, duk tsimin da ake dura mata,sai da ya Siga, kundai san sakwatawa da hade hade, wallahi haka deen yayi nasarar kawar mata da budurcinta, tun tana kuka, har ta daina kuka numfashinta ya rika fita sama sama, sabida taji jiki, ga budurci kuma ga magungunan da aka kimsa mata cikin ma wasu idan sun shigo hannunta a shara take zubawa, amma ta hadu hadi, ke in takaita muku saida deen yayi kusan awa daya da rabi akan nazia yana abudaya,Kuma ba wanda ya gaji cikin Su bare yayi kokarin hana daya, ba wanda yana da aure, qarar wayarshine ya mayar dasu halinda suke ciki, abu na farko da yazo mishi shine yayi zina da matar aure? Subahanallahi...?

ASHE KAINE MIJINA - 42

Bayan sun mini nasihohi aka kwasheni sai gidan mijina, su zainab khalifa da fatima duk an kawo jiki ana jiran ango da abokan ango Suzo ko za'ayi sa'a asamu wanda zai taya, amma har gurren 12:30 na dare ba ango ba abokanshi haka suka gaji da jira suka tafi gida, suna cizon yatsa" nima jabo zeek alifa ta bani tausayi danaga kwalliyar data chaba.

Naziah dai haka ta zauna jugum sunaa fita ta kulle daki, dan ta cika alkawarin deen dinta, Nayi bacci na, ga zafin da gabana yake min na wahalar da deen ya bani, cikin bacci nayi ta mafarkinsa.











Ji nayi an bubbuka mini kofa, in fito ashe har 11 na safee yayi, na fito wai zamuje walimar da akeyi bayan amarya da ango sunyi  na buka gafa ni wallahi banida lafiya!! akayi sama da kasa in zo muje naki zuwa suka gaji suka kyaleni, Bangaren nura kuwa yayanshi yayi rantsuwa idan har baije walimar nan ba sai yaci mutuncinsa, kuma bashi bashi har abada, dan ya zubar masa da mutunci iya zubarwa ranar daurin aure da baijeba, bama daurin aureba duk wani events da aka shirya nura bai halarci ko daya ba, haka dai ya shirya yaje walimar bada son ranshi ba wannan karon kuma ba amarya.

Walima tayi walima, an raba kayayyakin aure, gaskiya yayan nura mutumin kirkine kuma ya fitarda dan uwansa kunya, inaga walimar da akayi ba'ataba yin irinta ba duk sokoto, sabida komai need, anyi lafiya an kare lafiya an bar amarya da angonta da kuma halayensu...?

ASHE KAINE MIJINA - 43

Nura ya siyo wa matarshi sabuwar waya kuma aciki yayi saving din numbersa da sunanshi, koda bashida number ta amma ya mata letter yace duk duk abinda take buqata ta mishi sms a wayan da ya aiko ya ijiye mata akan hanyar dakinta.

Bangaren nura dana nazia daban ne, batasan shigarshiba batasan fitarshiba, haka shima, baisan chinta ba baisan shantaba, kullum yana manne dawaya yana waya da abar kaunarshi hulwaty azeez dinsa,.itama dai haka, suna farantawa juna rayuwa da kuma jaddada alkawuran da suka yiwa juna na kada ta kuskura mijinta ya kusanceta ita kuma tace kada ya kusanci matarshi.



Haka rayuwar aure ta kasance, mata tun tana kulle kofarta har ta gane cewa mijin nan nata yafita kiyayyarta, sabida haka saim ta dan saki jiki ta rage zaman daki tana zama parlour tayi kallon ta tayi chatting dinta, a groups chat, dama mayyar chatting ce idan sun hadu da m jabo a group din kar mu shagala ayita wasa da dariya kamar dama sun san juna su suke debe mata kewa, idan ana zolayarta da zancen banana takanyi murmushi aranta tace da deen dina bai dandana min ba ina har in koma ga mahaliccina indai akan wannan mijin nawane bazan san komai akan banana ba.

Gashi duk wani salon sarrafa namiji ta koyo shi sai dai ba mijin kuma bata bukatar sa a tunanin ta anyitane dan deen dinta....

SHE KAINE MIJINA - 44

Deen dinta, wasa wasa naziah tayi wata biyu gidan nura, kullum cikin liSsafi take, yanzu ya rage saura wata biyu ta kashe aurenta taje gurin abin kaunarta tanata shirya plane na yanda zata bullo ma abin ya sallameta cikin mutunci dan ta kula shima dan is ne.












Bayan wata biyu ne yayan nura ya shiya mana tafiya honey moon a turkey, Cyprus da India, nidai kam sai sms ya mini wai inje kaduna gobe amini  passport rt in shirya driver zai kaini, araina nace kuma uwar me za'ayi da passport har bazan je ba kuma Sai na tuna da yaya yace ko banyi dan kowa ba nayi dan yayan shi.

Munyi passport da komai, aka karbo mana visa da ticket da komai tafiya takankama na gama shirina koda ni ba son tafiyar nake yiba dan ina gudun achan ya sami sa'ata ya bata min shiri amma haka nayi biyayya ga karamcinda yayansa yake min yasa na amince.

Na fito parlour ina jira sai sms naji ya shigo "kije driver zai kaiki airport zanzo daga baya" araina nace tafi nono fari, na kira deen dina na gaya mishi zanyi tafiya yace shima zaiyi tafiya amma ya chanza bucking dinsa, naje airport driver ya bani dollars rapper daya nidai bansan ko nawa bane amma nasan suna da yawa, na saka jaka, har jirginmu ya kusa tashi baizo ba araina nace kardai ya wuce cikin jirgin ban ganshiba tunda ba saninsa nayiba, nayi hanzari na shiga jirgi, ko minti uku banyiba da zama ba sms ya shigo, Bazan sami damar zuwa yauba, idan kin isa let me know! haushi ya kamani, ya zai turani wata kasa ni kadai, amma van damuba sabida nafi bukatar haka.

Na isa Cyprus lafiya, kasace ta arna ga tsadar rayuwa, dala 100 idan na fitar ko abincin kirki banaci in koshi da ita, ni kadai nake holewata, na sayi sim guda biyu daya a dayar wayata daya a tablet dina, na kira deen dina na fada mishi na iso lafiya, na kira iyayena na gaya musu na iso lafiya, layin da nake kiran deen daban wanda na kira gida daban, ban kira nura ba dan banida Lokacin sa, sati na daya a Cyprus deen dina ya bakunci kasar, tunda yazo muke tare dashi ya mayar dani kamar matarshi, gabaki daya na tare hotel dinda ya kama ina honey moon dina dashi mai makon mijina na sunna, sau dubu sai mun kare lalartamu deen yake kukan abinda ya aikata ni nake karfafa mishi guiwa garin karfafa guiwa ma sai na kara bashi kaina akoma ruwa nariqa na gama da rayuwar deen na Sangartashi da kaina, yanda bazai taba iya rayuwa da wata mace idan baniba, Tir da halinki naziah....?

contact-form




Post a Comment

0 Comments