f Mijin Babata Ne 21 To 30

Mijin Babata Ne 21 To 30

 


Mijin Babata Ne 21 To 30


PAGE  21 TO 25

Dariya suka sheƙe dashi suka tafa, Aisha wani shu'umin kallo tabita dashi. Aliyu bazan taɓa yarda dakai  ba yanda kakeson matar nan naka, in ɗauko ƴar mutane abaka,ƙilama kun hada bakine kai da ita a dauko ta ku azabtar da ita,ku maidata bora, abinda nasani kawai zaka iya rubuta ta kaddan saki,inkai wa mahaifinta ya samu wani ya bata,don bazatai ta zaman jiran gawon shanu ba. Cikin haɗa rai take magana,babu alamun dariya ko wasa a tattare da ita. Subuhanallah, ni Aliyu naga ta kaina, komai zance ma Ummie da wiya ta fahimce ni,don na ɓata rawana da tsalle,dana amince da wasiyar mahaifina da duk haka bai faruba,da yanzun gida biyu maganin gobara.






A ƙasan zuciyar shi yake wannan maganan. Miƙewa Ummie tayi tana ƙoƙarin shigewa cikin gida,yai saurin ruƙo saleɓen zanin ta,tsayawa tayi cak batare da ta kalle shi ba. "Ummie pls forgive me. "Aliyu ka kiyayeni, kabani takaddan saki kawai,kaje ka zauna da wacce ka zaɓi farin cikin ta fiye da nawa".

Cikin fushi take maganan. Gaban shi tsananta bugu yake,yaune rana na uku da ya taɓa ganin mugun ɓacin rai fuskan mahaifiyar shi,gaskiya na tafka babban kuskure ya faɗa a ƙasan zuciyar shi. Azahiri ƙara marairaice murya yayi yace,"Ummie na kiyi haƙuri. To Aliyu ɓace min daga gani inka ƙara zuwa min da maganan nan ranka sai yayi mugun ɓaci". "Tou Ummie insha Allahu. Miƙewa yayi jiki a saɓule yai mata sallama,ya tafi yana tunanin mafita, lokaci ɗaya kuma yayi murmushi.

Kan kuce mai har ankai ma mai gari labari, take ya buga waya zuwa birni akaturo masa yan doka. Ɓangare guda ko Tani ta rinƙa yaban ruwa Hansai na watsa ma JIDDA amma ko kaɗan bata dawo ba,alama dai rai kamar ya fita. Zarah tayi yunƙuri guduwa mata suka riƙe ta masu jin haushin ta suka naɗa mata bugu tsiya,sai da ta kasa tashi, ana haka yan doka sukazo suka tafi da ita ,yayinda suka ɗau JIDDA, zasu kaita asbiti, su Atiƙah sai kuka suke. Sai da suka fara kai Jidda asbitin UDUTH kafin suka wuce da Zarah police station bayan sun bar Jidda da police mace guda da Hansai da Tani.






Dady wai ina zamuje ne. Cutie take magana ta nade hannuwan ta cikin riga da wando yellow purple ɗin ɗan ƙaramin hijjab yasa mata da takalmi purple,akwatin ta yake sa mata kaya.

Weekend zamuje,ran sunday zamu dawo sabida school. Ya faɗa batare da ya kalle ta ba yaci gaba da sa mata kayan a ɗan akwatinta. Tsalle tayi da murna,ta hau bayan shi tana dariya. Dariya yayi shima daidai lokacin yana rufe akwatin. Dauka yayi suka fito riƙe da hannun juna. Daidai lokacin tafito taci uban ado kamar bazata mutu ba,kallon kallo sukai ma juna,yawani murtuke fusa, yayin da ita harare ta galla masa. Good morning momy".

Faɗan Cutie da ta tsare Abeeda da ido. Batare da ta kalle inda take ba taja dogon tsaki ta wuce ta fita ba tare da ta ko gaisheshi ba. Murmushin takai ci yayi tare da shafa kan Cutie. Cutie ko jikin ta duk yayi sanyi. Koda suka fito harta banka ma motor ta wuta ta wuce. Aliyu ko matuƙar mamakin halin Abeedah yake.

ALIYU INA ZUWA HAKA.

SHIN WANI HALI JIDDA TAKE,TA MUTU KO TANA RAYE.

WANI HALI ZARAH TAKE.

DAMA ASHE ALIYU BA AURAN ABEEDA KAWAI YAKE DASHI BA.

PAGE 26 TO 30

Aliyu ko matuƙar mamakin halin Abeeda yake, da kafin suyi aure ba ƙaramin biyayya take masa ba kamar zata maida shi ciki, ko kaɗan bata son ganin ɓacin ransa,amma yanzun dattin ɗakin ta yafishi daraja a idon Abeeda. Mahaifin Abeedah ko duk hayaniyar da ake yanaji,bai iya kukan zahiri sai na fili,jikin sa ya tsanan ta da zafi, gashi babu mai temako akusa, don har ya cire rai da ita,jin ana faɗin ta mutu. Addua yake a zuciyar sa Allah ya saka ma Jidda, shi kuma Allah  yakawo masa ɗauki a rayuwar shi,in kuma lokacin sa yayi Allah yasa ya cika da kalman shahada.






Zarah ko nacan police station tana amsan azaba kala kala, duk marasa imanin police ɗinnan sun gama ƙara canja mata kama gaba ɗaya. Saida likitochi suka kwashe awa uku akan ta kafin sukayi nasaran dawo da numfashin ta, don dogon suma tayi lokacin da Zarah ta buga mata sandan. Don ko su kansu likitocin har suncire rai da zata shi,duk da akwai alaman rai atattare da ita. Hansai ko hankalin su duk a tashe yake tunda sukaji shiru ba wanda yafito balle suji tana raye ko ta mutu. Tafiyan awa biyu da rabi yayi daga shi sai yarshi komi ta gani a hanya sai tace Dady saya min, ko kuma ta tambaya miye wannan,wani yabata amsa wani yai murmushi yaja mata hanci,hartai bacci ta tashi tace,"Dady bamu iso ba. Murmushi yayi ya shafo kanta da ɗanyan hannun shi yace,"mun zo mana yanzun zamu ƙarasa". Gyaɗa kai tayi ta kwanta taci gaba da wasa da yatsun ta kamar wata babban mace.

Cute kenan akwai manyan ce kamar wata ruƙon tsofaffi. Parking yayi a dai dai killan gidan su mahaifin shi ba kowa  a a wajan sai bisashe da suke ta kiwo, yara ne daga can nesa suke wasan su, kulle motor dayayi ta hanyar danna key yasa motor tai kuka, take yaran hankalin su ya dawo kan su. Zuba musu ido sukayi, shiko ɗaukan Cute yayi suka fara tafiya,yaran ko zuba musu ido sukai kamar sunga tv. Assalamualaiku",sallama ya rinƙa kwaɗawa,amma ba kowa shiru,har ya juya zai fita,ya lura da Sa'ina dake zaune ƙarƙashin dalbejiya tana damɓara kwalliya kamar wata jaka yasa ran shi ya ɓaci.

Cutie ko tana arba da ita dawani saki ƙara ta ƙanƙame Aliyu,tana faɗin Dady dodo. Lokacin Sa'ina ta ɗago ta kalle su tawani saki baki da hanci. Shafa kan Cutie yayi yace,"ba dodo bane, yar iska ce. "A'a Dady. Aliyu ko wani mugun kallo ya watsa ma Sa'ina kafin yace,"ke mahaukciya baki iya amsa sallama bane. Washe haƙora tayi da sukai ja kamar ma aikatan cokula tace,"Ali banji bane. Ɗan tsaki yaja yace,"dalla ina Abba. Taɓa baki tayi tace,"yana ɗaki. "Ni kike taɓa ma baki, shegiya mai suffan buranya,inna ƙaraso sai na karya ki.






Ranshi ɓace yake maganan. Shiru tayi tai muƙus don tasan shi da rashin imani yanzun sai ya nema ya karyata, gashi tana shirin zuwa wajan saurayin ta. Dogon tsaki yaja ya nufi ɗakin Abba, kwance yake jikin sa ne kaɗai ke rawa gashi yai fitsari da kashi ɗakin duk ya ɗume da wari, ga yunwa naci cikin sa. Har Aliyu ya tusa kai yai saurin dawowa baya yana toshe hanci. Ke da mutum a ɗakinnan? ya tambayeta cikin tsawa. Jiki na rawa tace "yes baida lafiya ne Jiddah ne ke kula dashi. Ina Jiddah take da bata gyara shiba?,maike damun shi. Lokaci ɗaya ya jero mata wa ƴannan tambayoyin. Jidda an tafi da ita asbiti tun jiya baa dawo ba. "Miya faru da ita.

Dama-dama tawani fara kame-kame. Zaki min magana ko sai na taka ki mai suffan burai. Dama Zarah ne, nan ta kwashe abinda ya faru  ta gaya masa,ransa yai mugun ɓaci sai huci yake kamar ya daki babu. Ke to uban miye amfanin ki da bazaki dubashi ba banza ballagaza wanda tasha a mama, dalla tashi kije ki gyara shi tas.Yanda yake ihu yake tada jijiyoyin wiya ba ƙaramin razana tayi ba,jiki na rawa ta miƙe ta nufi ɗakin Abba yaune rana ta farko kenan da tunda ya fara ciwo shekara huɗu kenan bata ko leƙa shiba ta ga yayake. Azuciyar ta kuwa tsine ma Aliyu kawai take, toshe hanci tayi tana tsoron ta fita ya kileta,gashi saida tayi wanka  taci kwalliya zaisa ta aikin kashi tou ita ta yaya ma zata fara. Ƙwafa yayi ya samu turmi ya zauna ya ɗaura Cutie kan cinyarshi da tuntuni tawani ƙanƙame shi, a zuciyar shi ko ganin rashin kyautawan shi yayi da har ƙanin mahaifin sa ɗaya tilo da ya rage masa a duniya  yana ciwo bai san ma yanayi ba, gashi yana da halin temakon sa, rabon sa dashi tun ɗaurin auran sa da Abeeda ko ban gajiya bai samu zuwa yayi masa ba, sabida kunyar da abinda yai masa.

Tana kuka wi wi wi tana sharan majina, kwalliyan ta ƙara dame fuskan tazama kaman buranya ta ɗebi ruwa ta gyara shi ta canja mai kaya,duk da sunyi dauɗa acikin su ta samu wasu ta sauya masa ta fita da kayan can. Fitowa tayi tace mai ta gama, sauke Cute yayi ya miƙa mata wayar shi yace tayi game. Ɗakin ya nufa,ba ƙaramin tausayawa Abban nasu yayi ba ɗaukan shi yayi ya fito dashi yakai sa motor Cutie na biye dashi, abaya ya kwantar dashi yana hawaye yayinda suka shiga gaba shida Cute.





Cuty tsura masa ido tayi na seconds kafin ta kai duban ta kan Aliyu tace,"Dady waye shi. Cutie Baba nane, sunan shi Abba, ke kuma Kakan ki ne. Yana juya motor yana mata magana. Cikin mintina ƙalilan ya harba  motor kan titi sai cikin gari.

NAGODE SOSAI DA COMMENTS ƊINKU ALLAH YABAR ZUMUNCI

PAGE26 TO 35

Cikin mintina ƙalilan ya harba motor kan titi sai cikin gari, asbitin daji yakai shi wajan wani abokin shi Dr Munir inda aka anshe shi aka shiga dashi don bashi temakon gaggawa. Ɓanagaran Jidda ko likitoci bayan sunyi nasaran cetou rayuwarta suka fito inda suka kira Hansai da Tani sukayi masu bayanin ta farfaɗo,amma basu san lafiyan kanta tana cikin hayyacin ta ko ta samu taɓin ƙwaƙwalwa sai ta farka daga bacci tukunan zasu iya gane haka, da ta farka su tabbatar da sunzo sun gayama likita,don a ƙara dubata, su ci gaba da addu'a, godiya sukayi suka tashi suka nufi ɗakin da aka kwantar da ita. Zarah ata ko ina jin jiki takeyi, tun balle da akace yar kishiyan ta ta kashe,hatta wa yanda aka haɗa su cell ɗaya gana mata azaba sukeyi.

Duk ƙiban nan ta zaizaye ta rame tayi zuru-zuru kamar wata jaɓa. Hajiya Abeeda ko bata damu da tasan inda mijinta da ƴarta suka je ba, ta shiga cikin gari abinta, taje gidan wannan ƙawa taje na wancan, su kwashi jiki su bi can ta saki baki tana ta basu labarin mijinta. Ke mai bakin surutu tsiya daga ina, ina Abeeda, ko Aliyun ne ya kawo ki. Ummy ce kema Cute magana da ganin ta kawai tayi agabanta batare da tasan sanda ta shigo ba don harta bata tsoro. Turo baki tayi ta yamutsa fuska kamar zatayi kuka ta hau kujera tare da kalmashe ƙafa tace,"Ummy yunwa. A taƙaice tayi maganan. Buɗe baki Ummy tayi  kafin tace,"kaji min yar jakan uwa, ni zaki turo ma baki kice min yunwa. "Ummie yunwa, ta ƙara maimaitawa a taƙaice.








Zo cinye ni, tunda ninayi miki magana baki ban amsa ba kin shigo kamar wata aljana wai Ummy yunwa. "Dadyne fa ya kawo ni,yace ince miki banci abinci ba. "Ina Aliyun, "Ya wuce. "Tashi kije kitchen kice Sadiya tabaki abinci. Tashi tayi da gudu ta nufi hanyar kitchen. Aliyu ko bazama yayi police station neman Zarah tanan ne zai iya gane inda yarinyar take. Saida yaje police station uku ana huɗu ne  ya samu nasaran ganinta. Sanda aka fito da ita zuwa bayan kanta inda zasuyi magana. Zarah ƙasa tayi da idonta tana hawaye dama can shakkan Aliyu take don baida mutunci ko kaɗan tsaye tsaye yake mata magana babu ko kara.

Gwaggo nazo ja miki kunne ne wallahi,matuƙar yarinyan nan ta mutu ko wani abu ya sameta wallahi tallahi billahillazi ko duka arzikina zai ƙare, sai na ƙarar don inga an hukunta ki,baruwana da ke yar kakana ne, sannan mijinki kawunane mafi soyuwa a gareni zan rufe ido a wulaƙanta min ke,police kuci gaba da hukuntata. Cikin kakkausar murya yake mata maganan yanayi yana murza yatsun sa suna ƙara,iya abinda ya faɗan kenan  ya ciro rafar ɗari biyar ya aje musu akan tebur ya juya yabar wajan. Duk wani dake tsaye a wajan  saida yayi mamakin maganganun shi, sannan ya aje uban kuɗi ya tafi. Zarah ko duk ta rikice tasan halin Aliyu saide bai furta ba sai  ya aikata,tayaya asirin da tayi mai na bazai ƙara waiwayan ƙauye ba ya karye har yazo, dole takoma wajan mallam,don maganin ɗan iskan yaron nan.

Acikin zuciyarta take wannan maganan,duk da ana dukan ta amma saƙa mugunta take a ƙasan ranta. Nan ko police sun samu abin nema take suka ɗauke kuɗin suka tasa ƙeyarta ana bugu har cikin cell. Kai tsaye uduth ya nufa, da kwatancen da police sukayi masa  ya isa ward ɗin da take. Tura ƙofar yayi ya shiga da sallama. Hansai da Tani ansawa sukai suna duban mai shigowa. Sannun ku babaa, ya mai jikin. Yai maganan yana kallon gadon da take kwance ɗaure da roban ruwa,tana bacci gwanin ban tausayi,ga kayan jikinta duƙun duƙun,lokaci ɗaya yaji  tausayin ta ya shiga jikin sa da jijiyar sa.






Mai akace damuwar ta, Yatambaya akaro na biyu. Nan Hansai tamai bayani,bai wani gamsu ba, yafita ya nemi likita ya ƙara yi masa bayani, kafin ya fito yaje chicken republic yayo take away yakai musu, har lokacin bata farka ba. Inda Abba yake ya koma, lokacin har an gama dubashi an kwantar dashi shima sai bacci yakeyi, wajan likita yaje yamai bayanin hawan jinine yai sanadiyar kawo mai mutuwar jiki, rashin kulawa da zuwa asbiti yasa jikin sa ya mutu gaba ɗaya. Dr Munir yabashi tabbacin zai iya tashi, inde aka dage masa da gashi. Sallama sukayi ma juna bayan an samu mai kula da Abba namiji, zai biyashi.




    



Post a Comment

0 Comments