f Mijin Babata Ne 57 To 65

Mijin Babata Ne 57 To 65



Mijin Babata Ne 57 To 65



PAGE 57 TO 60

Jikin ta a sanyaye a hankali ta buÉ—e baki tace,"Yaya kayi haÆ™uri wallahi ban san ranta zai É“aci ba harta yanke É—anyen hukunci haka akan ka, don girman Allah kayi haÆ™uri ka yafe min".Ta Æ™ara she maganan da muryan kuka,ji yayi duk ba dadi lokaci É—aya a zuciyar shi,tayi matuÆ™ar bashi tausayi yanda take maganan. Dukawa yayi yana fuskan tan fuskan ta, sa hannun shi yayi a hankali kan lallausan fuskan ta  ya share mata hawayen da suka zubo yana murmushi kamar bashi aka gama kashe da mari ba yace,"Æ™anwata karki damu Ummie zata sakko zanje in bata haÆ™uri.

Yauwa abinda yakamata kayi kenan gadanga,fushin mahaifiya, bala'i ne da masifa akan É—anta,hatta Allah fushi yake dakai in kasa mahaifiyar ka cikin kunci tashi kaje kabata haÆ™uri,don gujewa fushin ubangiji. Fadan Iya da take tsaye ta bayan su tun É—azun da sai yanzun tayi  magana. Murmushi yayi yace,"zan bata haÆ™uri Iya,Ummy ta mai fahimta ce da haÆ™uri, nasan zata haÆ™ura. "Yauwa tashi kaje. Fadar Iya akaro na biyu. Mikewa yayi yana fasha fuska, tare da riko haÉ“an ta yamikar da ita.







Cute da gudu ta taho wajan sa ta kan kame shi, dukawa yayi ya dagota ya shillata sama, sukayi hanyar bedroom din Ummy, yana rada mata magana akunne tana gyada kai tana murmushi. Abeeda wai ke bazaki bikin kanwar Najaatu bane a katsina, ki tambaye mijinki, in zai barki. Fadar Aisha da suke zaune wajan shaƙatawa,suna ciye ciye, duk sunci ado kamar bazasu mutu ba. Kam bala'i da yasani da kar ya sani uwar su ɗaya uban su ɗaya, kayan ankon ma na wajan ɗinki, tafiyata zanyi,aini aduk fitata ban jiran umurnin Aliyu inde zan jira umurnin sa to bazani ba, kulle yake min kamar matan mallam,ban ɗauka ba kuma bazan ɗauka ba yasani ,banda lokacin sa.







TaÉ“a baki Aisha tayi cike da mamaki take kallonta ita ta isa tafita gaba gaÉ—i  batare da sanin Abubakar ba da ta kwana gidan su, bikin nan ma ya tubure yace baiga uban da zataje yi ba biki katsina bikin Æ™anwar Æ™awan Æ™awa cabÉ—i."Azahiri ko tace,"ai da yaganki sakwa sakwa rainaki zai rinÆ™a yi,mazan nan in baka nuna musu kaima jan wiya ne kana da taurin kai ai sai sharan gidan ka yafika walwala. Kide bari Æ™awata,ni wallahi ko ya mantawa nakeyi ina da ita, don shike mata komi, kwana biyu ma ban ganta ba ko tana gidan uwarsa ne oho, duk inda yakaita shi ya jiyo bani da asara".

Lallai lamarin Abeeda yana matuÆ™ar ba Aisha mamaki itade duniya kawai tasa agaban ta, wani kallo Aisha ta watsa mata a zuciyarta tace yar wahala, kibiye ma matan bariÆ™i sunan ki bazawara wata rana,bakina ganin yana Æ™aunar ki bazai iya turaki gidan ubanki ba,ni naiman haihuwar ma muke ido rufe bamu samu ba keda yake jaka ce kin samu kina wulaÆ™antawa,azahiri ko haÆ™ori ta washe tace. kawata aikin ki nakyau wallahi, karki yarda ko Æ™ara haihuwa balle harki tsufa,atara miki yaya ,shikuma yaje ya kara aure. 






Kaɗa manyan idanuwan ta Abeeda tayi kamar zasu faɗo ƙasa tace,"aure ai wallahi Aliyu bai isa ya auro wata yar iska ba, yamin alƙawari dagani babu ƙari, ke in taƙai ce miki Aliyu bai iya haɗani da kowa a zuciyar shi balle har yaji shaawan yimin kishiya, haihuwa ko bazan iya buɗe mai ƙafa ba kullum yaci kamar yasamu shinkafa, ke in taƙaice miki ancire min mahaifa,yanda bazan haihu ba kwata kwata,inci duniyata datsinke da kyau,ba wanda yasani sai ke da yau na faɗa miki don kema ƙawar arziki ce baki bani shawaran banza ".

Boye mamakin ta Aisha tayi da yacika zuciyarta lallai Abeeda ba Allah sam a gabanta,sheÉ—an yayi mugun buga mata gangar mu'azu tayi nisa banta jin kira a zahiri ko tace. Shegiya Æ™awata aikin ki na kyau sosai. Dariya suka fashe dashi tare da tafawa. Aisha na mata kallon sakarya. Atika Atika ke AtiÆ™a tashi ki daukan min tallan kokon nan rana nayi. FaÉ—an Zarah  tsaye kan Abeeda da tayi  É—aiÉ—aya kan gadon kara kannan tugu-tugu ba kitso, mika tayi ta mike tana gantsaro yan matasan nonon ta da suka  É“ullo kamar kan gero, suma azaban taÉ“awan maza ne yasa suka fito,turo baki tayi tana bin Zarah da wani mugun kallo tace.

Zara kin raina min wayo da yawa,ina bacci zaki wani tasheni akan banzar kunun ki ni bazani ba ki É—auka da kanki kije ko kijira yar iskan can Sa'ina  tazo ta je miki don wallahi bazani ba. RiÆ™e baki tayi tanabin AtiÆ™a da ido harta dasa aza tace,"kaji min shegiya yar iska nizaki gayama bazakije min tallan koko ba lallai wiyan ki ya isa yanka. Wallahi Zarah ko shure shuren mutuwa kike bazani ba, zaki zubar min da aji talla Allah ya kiyaye wallahi in zaki jira Jidda ta dawo  taci gaba miki ita ce bautantar ki amma bani ba,in kin matsy kije da kanki.







Tana kai aya ta mike ta shige bayi batare da ta É—auko buta ba. Tura Æ™ofar suka tura a hankali suka shiga tana zaune bakin gado tayi tagumi lokaci É—aya ya É—uÆ™a guywowin sa a Æ™asa ko É—agowa ba tayi  balle ta kalle su, lokaci daya  suka.

PAGE 61 TO 65

Tura Æ™ofar suka tura a hankali suka shiga tana zaune bakin gado tayi tagumi lokaci É—aya ya É—uÆ™a guywowin sa a Æ™asa ko É—agowa ba tayi  balle ta kalle su, lokaci É—aya  suka fashe da kuka lokaci É—aya a tare, don Aliyu yasan tun yana Æ™arami Ummy ta tsani kukan shi hankalin ta yanzun zai tashi ta shiga damuwa. Runtsa idon ta tayi tana jin wani abu yazo ya tokare  Æ™irjin ta sam batason jin sautin kukan Aliyu, lokaci É—aya ta maida kallonta kan Aliyu da Cute da suke kuka duk sun zuba mata ido.

Ya isa haka Aliyu" ta faɗa da ƙarfi cikin ɗaga murya. Lokaci daya suka haɗe kukan su kamar haɗin baki.

NIKO NACE LALLAI UBA DA ƳAR NAN TASHI ƳAN DRAMA NE, DAMA RAƊAN DAYAI MATA A KUNNE KENAN SUNA DARIYA ASHE DRAMA SUKA HAƊA

Kasan bansan ganin hawayen ka a kasa shine zaka zo ka tasa ni gaba dakai da mai kama da kyanwar MRS BASAKKWACE da baÆ™aÆ™en idon ta kamar na  ZEERO kuna min kuka, kutashi kuban waje in kuka zakuyi min kuma ka tafi da Yarka can ku Æ™arata. Cikin É—aga murya take maganan.






Cikin marai raicewa murya suka haÉ—a hannuwa suka ce," sorry UmmY,  a taÆ™aice. Shiru tayi bata kalle su ba, bata kuma basu amsa ba. Cute sauka tayi ajikin Aliyu tasa guywowin ta a Æ™asa ta kamo Æ™afar Ummy É—aya da yake Æ™asa tace,"Ummy Dadyna bazai Æ™ara ba wallahi, kiyi haÆ™uri, kinga Dady ma yayi kuka".

Maganan taso taba Ummy dariya amma ta danne dariya tace,"tashi kiban waje ko inyi ball dake mai bakin tsuntsu kawai, nayafe masa na haÆ™ura haÉ—a kayan ki kukoma gidan ku, maza tashi kikira Iya ta haÉ—a miki  kayanki  don banson takura. Kumburo baki Cute tayi kumatun ta suka  Æ™ara cikowa kamar na LIPTON GIRL tacewa,"ni anan zan zauna Momy ta bata son. Saurin toshe mata baki Aliyu yayi yace,"mata kull yana girgiza kai,kar na Æ™ara ji yanada nake son ki haka Abeeda kinji. GyaÉ—a kanta tayi.

Ummy ko tausayi yar jikan tata É—aya tunÆ™wal take bata  ace ka haifi É—a kamar ka haifi É—an shegw baka iya kula dashi balle kanuna  masa so wannan wata irin ballagazan uwa ce. Ummy kinyi haÆ™uri ko faÉ—an Cute  davata kafeta da ido.






Eh nayi badon halin ki ba da ubanki, tashi kije ki ce Iya ta baku abinci keda Auntyki JIDDA".Tashi tayi cike da farin ciki tai ma Ummy kiss a gefan kumatun ta ta fita da gudu cike da murna. Harara ta galla ma Aliyu da kan shi ke Æ™asa tace," wato ka raina ni baka É—auke ni da mutunci ba ko da matsayi shiyasa zan maka magana kasa takalmi ka shure maganata katafi lafani don baka da kunya kaje kace ma Ibrahim maine yayi haÆ™uri yabaka JIDDA koko to wallahi sai kabani takaddan sakin ta don ko Ibrahim bai isa ya hanani ansan takaddan sakin JIDDA a hannun kaba, don haka ka gaggauta katashi ka kawo min takaddan sakin yata JIDDA don amana uwarta tabani ita don  kawai anfi Æ™arfinane na haÆ™ura".

NIKO CIKE DA MAMAKIN MAGANAN UMMIE NAKE DAMA JIDDA MATAN ALIYU NE?, TO TAYA HAKA TAFARU BAI ZAUNA DA ITA BA YA AURE ABEEDA BISA DUKKAN ALAMU ABIDA BATA SAN DA WANNAN JIƘAƘƘAN A ƘASA BA, RANDA TAJI KO AKWAU ƘURA A ƘASA.

Tunda Ummy  tafara maganan saki yaji kamar tana buga masa guduma akai a razane yake kallonta yana girgiza kai. Wallahi Aliyu ko mi zai faru sai ka saki JIDDA wato kun haÉ—o baki da matar ka abaka ita kuje ku maidata boyi boyi ku bautar da ita, to bazan yarda ba aci amanar baiwar Allah ba marainiya. Cikin kakkausar murya take maganan tanayi tana murza yan yatsu.







 Aliyu ko sam a zuciyar shi bai ji zai iya sakin ta,don  zaman da sukayi da ita a asbiti ta shiga ransa,zai lallaÉ“a Ummie ta barshi da ita ko bazasu tare ba. Sosa Æ™eyan shi yayi yace,"Ummy itama ya kamata a samo mata malami da zai rinÆ™a mata lesson ta iya karatu da rubutu kafin akaita makaranta na boko dana islamiya".

BuÉ—e baki Ummy tayi lallai Aliyu ya raina ta wato tana gabas yana yamma duk maganan da tayi  masa bai ma shiga kunnesa  ba, wani magana ya kawo mata, Æ™wafa tayi ta tashi ta shiga ban É—aki, don bama tasan mai zata kuma ce masa ba. Murmushi yayi ya tashi ya fuce. Ba kowa  falon sai Æ™aran AC da TV  ga daining nan alaman anci abinci an tashi. Suna gama cin abinci Cute taja hanun Jidda wai suje  É—akin ta suyi wasa, hakan ko akayi JIDDA tabita bedroom É—inta ta kwaso kayam wasan da Ummy ta sayo mata ta baje a tsakar É—akin suka kama wasa JIDDA ko kamar saanta ta biye mata Cute sai farin ciki take.

Har ya shigo  basu sani ba hankalin  su ya É—auku wajan wasa,ya jima tsaye yana kallon su yana jin wani nishaÉ—i daÉ“a Abeeda ce da bazai taÉ“a tinanin Æ™ara zama da wata mace ba. Nima nazo ayi dani faÉ—an Aliyu,dukkan atre suka É—ago suka zuba masa ido cike.

!

Post a Comment

0 Comments